Author : Queenmerh Category : Complete Novels
daya zaune, ko kallon inda yake hamad baiba tubda ya dauke idanunshi harya shiga cikin dakin da sallama.
Anne ya hango kan abun sallah, bata tashi ba tunda tayi sallah ta dan nemi runtsawa a wajen.
“Anne…good morning ya mai jiki” ya fada ahankali gudun kar mara lafiya ta tashi.
“Morning dear, ya kuke kowa da kowa?”
“Duk suna lafiya” daidai nan ya karaso inda take ya zquna kan couch.
“Zuwan safiya haka hamad? Baka huta ba”
“Bazan iya hutawa ba ay tunanin halin da ku ke ciki bazqi barni ba, i missed you”
Shiyasa cikin jikokinta take bala’in son hamad ba kadan ba don ya fita daban.
“Toh ay gashi ka ganni saika zo ka tafi ko”
“Please anne karkice na tafi I won’t”
“Toh shikenan ay, wake son zaman asibiti allah na tuba inba dole ba.
Murmusawa yayi tare da aje mata bag din daya shugo dashi.
Anne tayi saurin kallonshi tace:
“Kaga tajudeen kuwa, tunda ya tafi sallah bai dawo ba”
Shuru hamad ya danyi kamar bazaiyi magana ba chan yace “na ganshi zqune a reception kafin na shugo”
“Jeka ce mashi ya shago mana, ko rintsawa yaronnan baiyi ba wallahi”
Kamar bazai tashi ba haka ya miqe tsaye ya nufi wajen kofar sannan ya futa.
Yanda yabar taj din haka ya taddashi a zaune ya dafe kanshi.
Rasa me zaice mashi hamad yayi, sai kawai yace
“Barka da safiya”
Dagowa taj yayi ya kalleshi kafin ya sauke idanunshi ya gyara zamanshi ya amsa shi babu yabo ba fallasa.
“Bismillah!!”
Ya mashi nuni da kofa, sannan ya juya ya barshi zaune.
Miqewa yayi shima a natse yabi bayan hamad din jiki a mace, koda ya shugo ita din ya fara kai idanunshi gareta, ganin yanda take barci peacefully yasa shi sauke ajiyar zuciya.
Tashi anne tayi ta dubeshi tace: “zan wuce gida akwai magunguna na daya kamata na sha, ka zauna da ita okay”
“Ya za a barshi shi kadai da…”
Dakatar hamad anne tayi tace “wuce ka kaini gida”
Tana fadin haka ko kofar magana bata bashi Damar yiba suka fice.
Suna fita anne ta dubi hamad tace “babu wanda ya kamata ya zauna da ita kamarshi, yafi kowa kusanci da ita saboda mahaifiyarsa ce”
Kalmar mahaifiyarsa saida hamad ya sake nanata ta zuciyarshi, shifa bai taba jin anyi maganar nanna tana da da ba,yadai san cewa ta taba aure sau daya kuma bata sakeyin wani ba bayanshi.He’s so curious da son jin wannan zance .
Bayan tafiyarsu ya zauna kan couch bini bini yake dagowa ya kalleta ya kasa samun natsuwa, ga tausayinta ya dameshi, tunowa dq ta dalilinshi take kwance ayanxu.
Kasa hakura yayi ya karaso inda take,kamar anne tasan he needs time with her, ya zauna kujerar dake gwfen gadon mara lafiya, samun kanshi yayi da kamo hannunta kamar wanda kejin tsoron tabata, ya riko hannun gam yana jin dumin mahaifiyarsa, wallahi irin wannan yanayin daban ne bazai misaltu ba.
Ya sumbaci hannunta ahankali ya soma magana yandq bazai tashe ba “aftaqiduk kthyran ya oummi, nayi kewarki sosai, i was blinded into thinking my life was complete without you, it was never, saima juyawa da tayi into miserable life, i had a traumatic days and night without you oummi, bansan dadin uwa ba,bansan yanda zan kalli cikin idanunki ba, i wish i could take out your pains that i caused you ya oummi, duk da an samin tunanin kinyi abandoning dina bana iya barcin kirki bana iya cin abuncin kirki ba tare da tunanin ki ba, shin a wani hali kike? Meke damunki? Meysa kika barni Baki waiwayeni ba? I was selfish all this time banyi tunanin ni wani hali na jefaki ba, ki yafeni ya oummi” yana magana amma baisan sanda ya soma jin lema lema ba akan fuskanshi, kuka da wuya ya sauka akan idanunshi amma akan mahaifiyarshi ya kasa controlling kanshi don she’s his weakness
Duk maganganun nan nashi a kunneta don tunda ya riko hannunta ta farka daga barci amma taqi nuna alamun haka, ka dumin hawayenshi na sauka kan hannunta daya rike she can feel how yanda yake trembling, ya Allah, zuciyarta na mata wani irin zafi ta kasa hana kanta hawayen dake sauko mata dukda bai lura ba. Abu kamar a mafarki haka takejin komai
Misalin wajen karfe goma da rabi sai gasu sun dawo asibitin,hamad, anty fadila, ya sameer.
Da sallama suka shigo dakin, yana zaune kan couch ya dafe kanshi da hannu daya,ya amsa sallamarsu sannan ya tashi zaune a natse duk suka juyo suka kalleshi,
Ya sameer ne yayi gyaran murya ya karaso inda yake ya miqa mashi hannu suka gaisa, anty fadila ta bishi fa kallo sosai, sai a yanxu ta kara tabbatar wa da dan nanna ne, don ga kamanninsu sosai ba kadan ba, da yanayin yanda yake magana da komai, dagowa yayi sukayi ido hudu dashi,ya gaisheta a natse ta amsa cikin mutuntawa kafin ta karasa wajen nanna.
Hamad dai na tsaye daga gefe ya nade hannayenshi a kirjinshi.
“Sannu Nanna…ya jikin? Allah yasa kaffara ne”
Bude idanunta kenan jin sallamarsu, Kallonta nannata tayi da idanunta da suka rine sosai suka fada tace “ku kira doctor ya sallameni”
Hamad ya futa don kiran doctor sai gashi ya dawo.
Ya sameer ya bar taj tsaye ya nufi nanna shima don yayi mata sannu. Shidai sunne kanshi kawai yayi kasa bai karasa ba gudun bacin ranta a natse ya futa daga dakin.
Dudubata doctor yayi don tabbatarta lafiyanta kafin ya kalli sameer “za a iya sallamarta yanxu, amma gaskia dole a kula da lafiyarta, kar a dunga bari tana shiga duk wata damuwa dazai janyo mata shiga shock irin wannan,“
“Thank you doc” Sameer ya fada yana miqa ma doctor hannu.
Ko kallonsu nanna batayi ba, gaba daya yanayin ta ya sauya kamar ba nanna ba, tayi wani irin fayau abun tausayi, kokarin tashi ta soma yi , jiri na dibanta,kayan da aka zo da ita dasu sune a jikinta,ganin yanayin da take ciki yasa anty fadila tayi saurin kama hannunta da babu canula a jiki ta taimaka mata.
Sameer da hamad suma suka mara masu baya.
Daidai nan ya fito daga office din doctorn daya bata sallama, da prescriptions din magungunan da zata buqata na qarin jini.
Nanna ta mashi kallo daya ta dauke idanunta suka fita daga cikin asibitin ita da fadila da hamad, uncle sameer kuma ya dan dakata.
Magana suka danyi da taj kafin ya futo shima suka shiga Motar da suka zo dashi gaba daya, suka wuce.
Suna barin asibitin anne ta kira sameer, yana dauka ya shiada mata an sallami nanna suna kan hanya ma,hamdala tayi kafin suyi sallama.
Babu wanda yayi magana tunda suka shiga cikin motar har suka iso gida, suna isowa suka wuce main house direct gaba dayansu banda hamad daya sake futa da motar.
Anne na zaune a sitting room sukayi sallama,take farin cikin fuskarta ya bayyana tayi saurin miqewa tsaye suka karaso inda take.
“Alhamdulillah!!! Sannunku da dawo ya jikin naki?”
Anne ta tambayi nanna tana kama hannunta suka zauna,murmushin yaqe kawai nanna ta mata batace komai ba sai ya sameer ne yace “ga magungunan da doctor yayi prescribing, sannan ya umarci a gujema duk wani abu dazai daga mata hankali”
Maganar da sameer yayi yasa anne ta dubi su shida fadila.
“Allah yasa kaffara ne, nasa ayi maku breakfast, Ina tajudeen din?”
Shuru duk sukayi gaba daya wannan yasa anne cewa , “barin shi kukayi achan?meysa?“
Bata gama rufe bakinta ba nanna ta miqe ta wuce sama don ko maganarshi bata son ayi.
Binta sukayi da kallo harta hau sama, wallahi duk ta zama wata iriya gaba daya kamar ba nanna ba.
Tana barin wajen anty fadila tayi saurin matsowa inda anne take zaune uncle sameer yayi gyaran murya yace “anne kun barmu cikin duhu, me….”
Saurin dakatar dashi tayi batama bari ya karasa magana ba tace “Zamuyi maganar daga baya, this is not the right time, jafaru ya kira maganar marayun da za ayi sponsoring karatunsu, ayi budgeting abunda ya kamata sai a sanar dani ”
Gaba daya suka hada baki wajen cewa “Allah ya ja da kwana ya kara arziki mai albarka su kuma allah yasa karatun ya amfanar dasu” ta amsa da ameen sannan ta miqe ta bi bayan yar uwarta rabi na biye da ita da warmers cike da abuncin, tuwo na musamman anne tasa a mata da miyar ganye saboda karin jini, da sallama ta shiga part din nanna, a zaune ta taddata bakin gado ta dafe kanta da hannayenta.
Koba’a fada mata ba tasan kuka take yi,nuni tayima da rabi ta aje warmers din ta futa, nanna najin sallamar anne kuwa tayi saurin goge hawayen dake fuskarta ta dago ta kalli anne.
Murmushi anne tayi mata sannan ta karaso inda take zaune ta dafa ta tace “hajara,”
Dagowa nanna tayi ta kalleta sai ga hawaye, ganin haka yasa anne saurin kokarin kwantar mata da hankali.
“Dan Allah kibar wannan hawayen, karya jawo maki wata matsalar, allah kadai yasan yanda kikeji aranki, amma ina rokonki da ki kwantar da hankalinki, ga abunci nan an kawo, freshen up saiki samu ki danci wani abun okay?”
Rabi dake zaune a sitting room din nanna tayi saurin shugowa bedroom din jin kiran da anne ta mata, tana shugowa ta wucewa bathroom kafin ta futo, “bismillah hajiya an kammala”
“Sannu rabi” nanna tayi magana dakyar.
Miqewa anne tayi ta futa “bari na barki zan dawo anjima”
“Toh anne” Nannata amsata
Tun bayan futar anne takai wajen minti talatin kafin ta miqe ta shiga bathroom ta watsa ruwa.
Bayan tafiyarsu jiki a mace ya shiga cikin motarshi, yafi kusan 30mins a zaune bai motsa ba, ya runtse idanunshi saboda wani irin ciwon kai dake damunshi tsakanin daren jiya da yau, kirjinshi ko har yanxu nauyi yake mashi.
Jiki a mace ya tada motar yayi reverse yabar harabar asibitin.
In less than 15min ya iso transcorp, ko iya parling baiba ya aje masu motar a wajen ya wuce sama.
Koda ya shigo dakinsa zama kawai yayi bakin gado ya dafe kanshi, wani irin zazzabin mai zafin gaske na neman dibanshi, kota cikinshi bayaji don rabonda ya sama cikinshi abunci ko ruwa tun dinner din da sukayi a gidan.
Zaman nan dayayi saiya zamana kamar bazai iya tashi ba saboda zazzabin gadan gadan ya taho mashi dole ya kwanta yaja duvet ya rufe jikinshi.
Anne na zaune kan couch ta jawo wayarta ta soma dialing number shi gar sau uku ba a dauka ba,gaba daya abunne babu dadi, tasan yanxu haka shima yana chan cikin wani hali, tund aga mahaifiyar tasa itama.
Yanda rabi ta aje abuncin nan haka ta dawo ta daukeshi don kwata kwata bata taba shi ba, saima kwanciya datayi anne ta shugo dakin saitayi tunanin ko barci tayi wannan yasa ta barta tadan huta.
Anne na fita nanna ta ta jawo hoton dake aje kasan pillow dinta, kurama hoton ido tayi sosai ta kasa daukewa sai hawaye…
40 years back….
Shekarar nanna goma chif a saudi, acikin wannan shekaru abubuwa da dama sun faru da ita, masu dadi da mara sa dadi.
Ranar da allah ya hadata da abdallah shine ranar data fara zuwa makka domin yin umra, don a madina take karatu.
Shigarta kenan ka’aba ta fuskanceta taji wani irin sanyi na dibanta, ranar ta kasance rana mafi sanyi ga wata ni’imatacciyar iska dake kadawa ko’ina kamar za ayi ruwa, gashi lokacin babu irin mutane sosai dinnan don babu cunkoso kwata kwata, take wani hawaye mai sanyi ya sauka kan fuskanta ayayin datayi ido hudu da dakin Allah ta fara dawafi, daidai wajen hajarul aswad ta tsaya tare da shafa wajen ta rufe idanunta, takai wajen minti biyu a haka kunnuwanta suka soma jiyo mata muryoyin dake gefenta saidai muryar mutun daya ce tafi zama a kunnanta inda yaketa yin addu’oi da larabci, saitaji gaba daya kamar ita yakema adduar, tana dena jin muryar tasa ta bude idanunta tare da kallon gefenta inda allah ya bata ikon ganin irin jakar maniyyata da suke sakawa, cikin hanzari ta dago ta dauka jakar tare da juyawa don ganin mai ita.
Saboda yanda kowa ke sanye da ihram yasa ta kasa gane kona wanene wannan yasa kawai ta rike ta cigaba da ibadarta.
Tana gamawa tayi safa da marwa ta sauke umra sannan ta wuce wajen da ake kai abubuwa idan sun bata.
Tana zuwa ta masu bayanin inda ta tsinta abun, wani dan paper form suka bata tayi signing ta saka information dinta don haka akeyi idan har mutun ya tsinci abu saboda gudun kar wani abu ya bata daga ciki, tana cikin rubutawa abdallah ya iso wajen.
Dake tana daga chan gefe wannan yasa batama lura dasu ba.
Tana gama rubutawa ta karaso wajen macen security din dake wajen ta bata paper din, matar ta soma zazzage jakar don shigarda abubuwan dake ciki, kusan kullum sai an samu irin jakar don duk maniyyata irinta suke amfani da saidai banbancin color.
Hajara dai na tsaye har matar ta gama shigarwa tana gamawa dake counter daya ne sai dai babu cudanya wajen mata da maza kowanne da bangarensa ta miqa bangaren maza, abdallah dake tsaye ya tabbatar da nashi ne aka duba id din dake ciki sannan yasa hannun tabbatar da babu abunda aka dauka a ciki, kafin aka bama hajara itama tayi signing.
Magana abdallah yayi da security din yayi mashi nuni da counter din mata adaidai lokacin ta dago bayan ta gama rubutun idanunshi ya shuga cikin nata, suka sallameta ta juya, shima ya karba jakar ya fita.
wannan ne mafarin haduwar taheel da nanna.
Duk wani abu da allah ya rubuta ko allah ya kaddara indai alkahiri ne saiya faru cikin kankanin lokaci, daga wannan ganin dayayi mata allah yasa mashi qaunarta a zuciyarshi, abunda bai taba ji ba,encounter dinsu na biyu shine ranar da aka gudanar da wani babban taro a makanrantarsu,cikin ikon allah kuma ya sake hadasu ta wata hanya daban, ita bata ganeshi ba don saida yayi mata bayani ta gane, baizo mata a matsayinshi ba, da matsayin da yake dashi a kasar yayi mata godiya sosai.
Daga wannan lokaci soyayya ta kullu tsakanin taheel da hajara, hajara itace mace ta farko da abdallah ya fara so, tsaftaccen so yake mata haka zalika itama take mashi,su a nasu aladar babu wani jan lokaci wannan yasa ya nuna mata aurenta yakeson yi, sannan ya buqaci ganin iyayenta.
Da farko nanna ta tsorata don babu wanda yasan dashi a gida sai anne, tsoranta na biyu shine aqidar babansu santuraki, idan mace ta gama karatu shike zaba masu mijin aure, kamar anne data gama karatunta already ya bada ita ga dan business partner dinshi.
With the support and courage din da anne ta bata kuma ta shige mata gaba suka sanarda mahaifinsu santuraki, daga nan mafarin tangarda ta shigo don santuraki bai amince ba, don itama ya mata miji, tana gama karatu.
It was a very hard moment for nanna don tana masifar son taheel,rashin amincewar iyayenta bazaisa ta aureshi ba, dole ta hakura da abdallah.
Ta shiga damuwa sosai ba kadan don anne ce kawai tasan wannan,karatunta ma duk yayi baya tayi wani irin rashin lpy sosai.
Tsakanin yan uwa sai Allah, halin da nanna ke ciki anne ma ta shiga amma dole ta hkura da zabinta tabi na mahaifinta amma bazataso yar uwarta ta shiga irin halin data shiga ba a baya wannan yasa ta sake tada maganar tare da rokon mahaifinsu, alhaji santuraki nada dogon buri da future akan yayanshi, but hajara failed him dalilin halin da anne ta shiada mashi take ciki wannan yasa ya yanke wani tsatsauran hukunci, inda ya yarda saidai ya shaida mata idan tayi regretting decision dinta she has to forget tanada uba.
Anne bata yarda ta fada mata wannan last furucin mahaifin nasu ba akayi auren abdallah da nanna.
Bayan aurensu da shekara guda allah ya azirtasu da d’a namiji inda yaci sunansa (Tajudeen abdullah taheel)abdallah yayi murna yyai murna mara iyaka ba kadan ba, adduar da ya dade yanayi allah ya amsa ta, ya samu magajinsa.
Bangaren nanna babu wanda ya kaita farin ciki itama,koda ta shaida ma anne itama tayi farin ciki sosai ba kadan ba, saidai a lokacin ne nanna ta fuskanshi har zuwa lokacin akwai matsala tsakaninta da mahaifinta, don har zuwa lokacin bai amince kuma ya karbi taheel a matsayin mijinta ba wannan kadai yasa ta kasa komowa gida don batasan da wani ido zata kalli mahaifin nata ba saboda bijire masa datayi ta dauki zabinta.
Anan gida nigeria kuwa, sharridan da santuraki ya gindaya ashe masu tsauri ne, inda ya haramta wa kowa kusantar nanna, koda ta haihu ma anne taso zuwa tare da mahaifiyarsu amma yace bai yafe ba duk wanda yasa kafa ya bita, haka suka hkura amma bata taba bari nanna tasan dalilin ba kenan.
Taj nada shekara uku mahaifiyarsu ta rasu, a lokacin ne nanna tasan duk halin da ake ciki, don mahaifinsu ya shaida mata indai tasa kafa tazo nigeria toh bai yafe mata ba.
Hankalin nanna ya tashi sosai don sai a lokacin ta tabbatar da akwai matsala babba tsakaninta da mahaifinta, kuma bai amince da aurenta da taheel ba har zuwa yanxu.
Tanaji tana gani ta kasa zuwa nigeria tayi kukan rashin mahaifiyarta data kasance itace mai tausasa ta da anne, mai nuna mata komai mai wucewa ne kuma komai daya faru mukaddari ne dağa Allah.
Akwana a tashi taj ya taso da shakuwa tsakanin iyayenshi, musamman nanna mahaifiyarshi, bashida hayaniya bashi da yawan surutu kwata kwata, da farko ma tayi tunanin ko yanada wani mental issue ne aka tabbatar masu da lafiyarshi kalau kawai dai miskilin yaro ne, bai cika wasa ba saidai kullum yana jikin mamanshi.
Taj na gab da shiga shekara bakwai a duniya komai yayi turning upside down on a blink of an eye, aurensu shekara takwas nanna bata taba sanin abdallah nada wasu iyali ba sai a lokacin.
Babu abunda abdallah bai dauke ma nanna ba, gida na alfarma, cima mai kyau, mota kayan jindadi na zamani daidai gwargwado kuma daidai karfinsa daya nuna mata.
Akwai wata ranar friday, nanna na zaune a sitting room tana kallon tv, gaba daya hankalinta ma bayaga tv don gaba daya wani irin faduwar gaba take ji cikin kwana biyu, tayi nisa sosai cikin tunani kamar ance ta maida hankalinta ga tv taga abdallah, janyo remote tayi cikin sauri ta kara volume don jin maganr da akeyi a jiki, take jikinta ya soma bari,ko barci take taji muryarshi zata iya farkawa.
Abdallah ne da kuma wata mata a gaba suna tafiya sai wasu manyan mutane dake biye dasu a baya suna zagayen shops din wajen a yanda aka