Author : Queenmerh Category : Complete Novels
shiada mata motar datazo jiya sun sake dawowa.
Tana shiga cikin gida ta kira hadiza, ta dunga Zazzaga masifa itafa wallahi idan aka kama jamilu bazata yarda ba gwara hadiza tasan yanda zatayi tun wuri, hadiza ta shiada mata wallahi babu irin tsoratar da sabeehar da batayi ba akan ta fada mata ko wani abun tayi aka korota ta shaida mata ita wallahi aiki kawai taje tayi suka gaji suka sallameta, jamila tace ay wallahi duk wadda kikaga an sallamota haka toh duk yanda akayi wani abu tayi.
“Amma jamila in wani abu tayi suke nemanta mutanen nan ba hukuma zasu saka a ciki ba?,kuma kince masu kudi ne”
“Eh kuma haka ne fa, ke harda wani balarabe fa toh kodai….kodai santa yake ne ya biyota har Nigeria?? Dan jamilu yace daga agencies suke wai, kuma wallahi wanda ke nemanta shi balaraben ne kuma dan sauudiyya”
Shuru hadiza tayi tana nazari tace, “kuma kince masu kudi ne?”
“Eh mana jiya kinga jibegegiyar motar da sukazo da ita”
“Ina zuwa jamila”
Kit ta kashe wayar ta futo zuwa kitchen bataga sabeehan ba ta zagaya backyard saiko ta ganta tan shanyan kaya.
“Ke zonan”
Aje bokitin sabeeha tayi tabi bayanta suka shiga daki hadiza ta dubeta tace “akwai wani wanda yace yana sanki ne achan saudiyyar kafin ki dawo?”
Cikin sauri sabeeha ta dago gabanta na faduwa, “ah ah” ta amsa ta a natse,
“Dan uwarki me zaisa wasu suzo nemanki anguwarmu? Eh??“
Sauke kanta kasa tayi tana nazari, badai taj ke nemanta ba? Ina babu abunda zai shashi nemanta.
“Ba magana nake maki ba kike sassauke kai kamar munafuka? Babu yanda za ayi wani balarabe yazo yana nemanki indai bakiyi wani abun ba, karuwanci kikayi achan??”
Cikin jin zafin maganr maman nata ta dago ta kalleta “wallahi mama ban taba yin abunda allah ya haramta ba ni bansan su waye ba”
“Na rantse da allah kika jawo min bala’i ina tsaka da jin dadin rayiwata tun ban tsufa ba allah ya daukemin talauci a wannan shekrar wallahi wallahi sai kin gwanmaci bin ubanki lahira,”
Tana gama fadin haka ta korata, sabeeha ta fita jiki a mace.
Yanxu idan mamanta ta gano cewa tayi aure a saudiyya fa? Idan ta gano abubuwan data boye mata ya zatayi? Innalillahi wa inna ilaihi rajiun, take gabanta ya soma faduwa tunawa da maganganun da mamanta tayi, ko ba a fada mata ba tasan taj ke nemanta, amma meysa zai nemeta? Batada wani alaqa dashi kuma, alqarsu ya gama yanketa tun kafin ta Sanyo kafarta a kasarnan ya mata kora ta wulaqanci duk halarci datayi masa.
Tana fita hadiza ta kira jamila, tana dagawa tace “jamila munafukar yarinyar nan taki fada min komai wallahi, …”
“Haba hadiza yarinyar nan tafi karfunki ne? Eyy?”
“Bari nasan dabarar da zanyi, baki cemin komai ba gameda shi wanchan”
“Shege yanata faman kirana jiya naqi dagawa dana gaji blocking din shege nayi”
“Amma bkya tunani zai iya jawo mana matsala jamila? Kinga yanxu…”
“Kinga dan allah kibar maganar wannan dan wiwi din, babu abunda zai iya, kuma ay baisan cewa…”
“Jamilaaa jamilaaa….” Jamilu daya bankadi dakin ya soma kiranta.
Saurin kashe wayar tayi tana kallonshi gaba daya sai warin rana yake tsabar an bugu.
“Da wa kike waya?”
“Hadiza ce”
“Mutanen nan bin yan unguwa suke suna bincike akaina, wallahi zan fada masu gaskiar al’amari ni banida wani hadi da ita”
“Haba mai gida, so kake ka tona mana asiri, ka manta kudaden da muka karba? Da albashinta da muka dunga karban kusan rabin kason kudin?”
“Toh hadizar fa? Kin fada mata me tace?”
“Ka zauna mana” ta fada tana kallonshi yanda yaketa faman gumi.
“Me gida banajin mutanen nan wani abu tayi masu suke neman, ni nafi zargin ko daya daga cikinsu ne tayi aiki a gidansu yake sonta shine ya biyota”
Dam gaban jamilu ya bada, idan bai manta ba da kanshi ya bada aurenta ba tare da tunani ko na sakan daya ba, kuma jamila bata sani ba kwata kwata, maquden kudade aka basu shida ogan agencies dinsu kuma suka raba a tare.
Toh kodai dalilin dayasa ake namanta kenan, bazia manta irin maqudan kudaden da suka raba ba shida oga har fili saida ya saya a duten habuja duk jamila bata saji ba badan kudin sun kare da wuri bama ta hanyar chacha da yakeyi ay da har aure zai karo.
Sai kawai jamila taga yana murmushi a ranshi yace “harka ta samu kenan”
“Yanxu dai kinsan inda hadizar take ko?”
“Eh har gidan naje wallahi”
“Toh ay shikenan” ya fada tare da wucewa daki, ko minti biyu baiba ya kwado mata kira aranta tace jarababbe.
Tunda ya dawo gida bai sake futa ba sai wajen karfe biyar, yana futa sabeeha ta lallaba ta wuce part din nashi, tayi abunda zata ta fuce.
Yana cikin workout cikin gym din daya fara zuwa wasu yammata sukazo inda yake tare da mashi sallama.
Irin classy abuja babes dinnan ne da sukagaji duniya sosai dan kowacce da yan kudadenta a jiki, ansha bbl duwawu tuku tuku kana gani kasan na natural bane ga attchment da sukaji akansu da suka daurama dankwali.
Sallamr da sukayi ne yasa ya aje abunda yake ya dago shi kwata kwata baima san dashi suke ba harya miqe zia bar wajen daya daga cikin babe din wadda tayi dayar kyau tace “hey!!!, can i have a minute with you”
Fuskanshi babu yabo ba fallasa ya tsaya ya kalleta daga yanda take magana ya gane irin matan nan ne da suke flirting da mutane.
“If you don’t mind can i have your digit?handsome?”
Smirking yayi kai tsaye yace “taken, excuse me please”
Yana fadin haka yabarau tsaye a wajen suka bishi da kallo, “teets daman na fada maki ba duka fararen nan ne masu son mata ba”
“Karya ne wallahi babu namijin da zai ganni baiji wnai abu ba”
“Okay then keep trying your luck”
“Kiji wai he’s taken?, ay wallahi ko mata goma ne akanshi teets saita sameshi,”
“Shegiyar gari” suka fashe da dariya harda tafawa.
Yana futowa daga wajen salim ya kirashi, ya shaida mashi yanda sukayi da agent din agency dinnan wanda ya basu information din jamilu.
Yana aje wayar ya sauke ajiyar zuciya beneth his breath yace “where are you? FATIMA…..?”
…
“Mama..ana kiranki a waya” dan jamila ya kawo mata, kallon wayar tayi ganin yaron ya dauka kamar ta kwada mashi mari tace “tafi dan ubanka bana hanaku daukan min waya ba”
Futa yaron yayi jamila ta kai wayar kunenta, dahiru yayi dariya yace “jamila kenan, tun jiya inata kira bakya dauka”
“Kai dahiru nifa matar aurece, kiran da kakemin bai dace ba karka sake kirana dan Allah”
“Ay baki isaba wallahi jamila, dole na kira ki dauka”
“Inkai ubana ne saika snai na dauka,kai wallahi jamilar daka sani a sa ba itace yanxu ba wallahi”
“Toh toh madallah, nace ba? Yar kawarki harta girma ashe? Ina nufin yarinyar da..”
“Dahiru…..!”
Ta kira sunanshi da karfi, “jamila kenan, kina tunanin zaku rufen baki ne? Kina tunanin na manta ne? Shekaru ashirin da doriya da suka wuce keda kawarki..”
“dakata haka ya isa, ay ban manta ba, bari zan kiraka anjima mijina ya dawo” ta kashe wayar kit…
Jamila fa har zufa take sosai, ada tayi tunanin ta raina mashi hankali ashe yasan me yake, ya zatayi da wannan shegen?”
Kiran hadiza tayi a waya “hadiza akwai matsala…”
After 2 days…
Kwanan rabi biyu tana zazzabi, ayyukan daya shafi gyaran sama sabeeha ce keyi, ita ke dafa abunci da ake yima anne da nanna na karin lafiya.
Tundaga ranar ta kara tabbatar da yarinyar nada kazar kazar, sannan tana da amana, don sau wajen biyu anne na aje kudi intentionally ko zata dauka amma ko mataar dashi ba a yi kwata kwata, gashu duk sanda zata gaishe da babba saita duqa har kasa saboda respect.
Lokaci guda anne taji yarinyar ta shiga ranta, nanna ko daman babu wanda zai yabi sabeeha kamarta.
Tana gama ayyukanta zata wuce dakinta ta zauna, kwata kwata bata yarda ta hada hanya da yan gidan, allah ya taimaketa ma suna hutun makaranta.
Bangaren taj ko duk sanda zataje saita ambula hijabi ta rufe fuskarta kwata kwata bata yarda ta bari ya ganta ba, kuma allah ya taimaketa duk zuwan da take dakinsa tana gyara basa taba haduwa.
Akwai ranar da suka kusa yin clashing shida ita, ta futo daga part din anty fadila datasa azo a dauki lunch dinshi rabi tace taje ta karbo saboda su laila basa nan sun fita.
Haka ta zumbula hijab taje ta karbo abunci sannan ta dawo, tana gab da bude kofar part din aka budo daga ciki, cikin sauri ta matsa tare da kauda fuskanta, kallo daya mata ya kauda kai ya wuce abunshi, ta sauke ajiyar zuciya tashiga ta aje sannan ta futo.
Kwata kwata bai taba kai attention dinshi gareta ba. Toh ta ina ma zai fara tunanin itace?
Cikin kwanakin nan taj yaje agency dinan yafi a kirga, da salim ya lura kamar raina masu hankali sukeyi suna karbar kudi dayaji haushi kawai yace ma taj babu kamshin gaskia atattare da mutanen, taj believed so aswell wannan yasa salim yayi threatening dinsu indai basu kawo jamilu ba zasu saka hukuma a lamarin, don gaba daya basu da gaskia.
Abokin jamilu kuwa dayaji yayi saurin kiransa ta sabon layin daya chanza ya shaida masa komai, jamilu fa ido ya raina fata, idan aka gano komai zai iya shiga matsala, gwara tun kan akaiga hukuma ya fada masu gaskiar shi bashida alaqa da yarinyar kuma ya kaisu inda take kar ace za a kamashi.
Waehe gari da safe da kanshi ya tafi agency, oga ya nemi salim a waya don ya bada katin sa, ya shiada mashi jamilu yazo, salim ya kira taj ya shaida mashi threat din da suka masu yayi aiki don jamilun ya bayyana kanshi, ko abunci kasa tsayawa taj yayi yaci ya futa.
Harya gane wajen don da kanshi yakai kanshi suka hade da salim.
Suna shiga jamilu yayi kuri kamar munafuki a zaune.
Oga ya kallesu yace “dan allah kuyi hakuri, kar kusa hukuma a ciki gashi nan wannan ne jamilu”
Salim ya dubi taj yace “this is jamilu,“
“Oga dan allah kuyi hkauri, dan darajar allah karku kamani”
Salim ya kalleshi yace “babu abunda zamu maka, tambaya daya biyu zamu maka”
“Kasan wannan yarinyar??”
Kallon hoton jamilu yayi yayi kamar bai ganeta ba
“Tayi wani laifin ne? Sata tayi ne? Kamata zakuyi?”
“Ah ah babu abunda tayi ka kwantar da hankalinka babu abunda zamu mata”
“Toh a gaskiya nidai ba marikinta bane,anguwwar mu daya nida mahaifiyarta wadda ta kasance kawar matata, toh shine daman ta nemi alfarmar a nema mata aikatau, saboda yarinyar bata da uba shine na rubuta nine marikinta”
Salim ne ya dubi taj ya mashi fassarar komai taj ya mashi magana da turanci shi ba wannan dogon bayanin yakeso ba, he wants to know inda take.
“Yanxu tana ina ita da mahaifiyar tata?”
“Sunbar anguwarmu kuma wallahi babu wanda yasan inda take”
“Ba kace mahaifiyarta kawar matarka bace”
“Eh…ay muma bamusan inda suka tafi ba”
Salim na fassara mashi ya runtse idanunshi kafin ya bude jijiyoyin kanshi na firfitowa he’s so fed up, he wants to find her, he wants to see her.
Shifa salim kwata kwata irin mutanen nan ba abun yarda bane, basa gane kowanne yare saida kudi, Ganin haka yasa salim cewa, “daga kan dubu dari biyar zuwa miliyan daya idan har kayi mana kokarin nemanta a duk inda take zamu baka abunda yafi haka ma”
Jamilu najin zunzurutun kudi haka ya bude idanu, kunenshi har motsi suke, salim na ganin haka yasan cewa duk munafukai ne.
“Toh zanyi kokari.. zan tuntubi matata, tunda tasan babarta sosai”
Murmuahi salim yayi ya fada ma taj komai, ogan agencies din yace “toh oga gashi mun kawoshi…za a bamu namu kason ko?”
Aje masu few notes sukayi sukabar wajen bayan sun bama jamilu card dinsu.
Jamilu bai taba sanin sanadiyar yarinyar nan zaiyi arziki ba auren da bai kara ba yanxu da kudaden nan zai kara saboda haka dole ya nemo masu yarinyar nan.
Washe gari yasa jamila a gaba, tun daren jiya yake mata sababi akan saita kaishi har inda hadiza take, tayi tayi ya fada mata dalili yaqi, karshe dai ya fada mata mutanen nan sunce zasu kawo hukuma idan har bai nemo masu inda yarinyar nan take ba.
Jamila najin hukuma hankalinta ya tashi, jamilu yace indai bata kaishi inda hadiza take ba saidai aurensu ya kare a anan dole ta shirya suka tafi ya hanata kiran hadiza duk asunan wai kartaji abunda ke faruwa ta dauki yarta ta gudu.
Motar haya suka hau shida ita har maitama, suna isowa estate din jamila tace “bazasu barmu mu shiga ba sai an kira daga ciki”
“Yanxu anan take? Hadizar da yar tata?”
“Eh”
“Toh me takeyi anan? Nadaisan duk danginsu babu masu arziki”
“Aikatau mana, aiki takeyi anan din”
“Toh shikenan muntafi kawai”
The next day..
Gaba daya ayau bai samu sun hadu da salim ba saboda asibiti daya kai anne treatment din da ake mata.
Basu dawo gida ba sai wajen yamma, har zuwa yanxu babu wanda yayi suspecting rashin lafiyar anne dagashi sai ita.
Kai tsaye ya wuce part dinshi ya dan kimtsa kafin ya futo ya wuce main house.
Yana shugowa ya wuce sama direct bangaren oummi, bakinsa dauke da sallama ya bude kofar sitting room, kamshin turaren wuta nee mai dadi ya mashi sallama,da yasashi sauke ajiyar zuciya,knocking din kofar dakin nanna yayi daga ciki ta bada izinin shugowa, kafin ya bude kofar, sabeeha dake tattara lunch din da nanna tasa azo a dauke tana jin sallamarshi gabanta ya wani fadi, allah yaso ta saka hijab dinnan saidai bata rufe fuskarta dashi ba, aiko wuff tayi saurin janyo shi wajen bakinta.
“Har kun dawo?” Nanna ta tambayeshi tana dubansa fuskanta dauke da murmushi, shima maida mata yayi da murmushin kafin ya amsa ta “eh”
“Hmm wannan futa da kukeyi daga kai sai anne cikin sirri ina fatan babu abunda kuke boye mana”
Ganin irin kallon da take mashi bayan tayi tambayar ne yasashi kauda kanshi, don bayason su hada ido don bayajin zai iya mata karya.
“Laaa oumi, babu komai, munje factory ne kawai”
“Toh ay shikenan in tayi tsami maji,kayi luunche?”
Girgiza mata kai yayi yana jujuya wayan dake hannunshi, yanda ta mashi tambayar nan yasan cewa ta gane suna boye wani abu shida anne.
“Fatima zuba mashi kafin a futa da sauran abuncin”
Tunda ya shugo baima lura da mutun a wajenba amma dayaji anne tace fatima sai kawai yaji yanason kai hankalishi zuwa ga wajen.
Sunne kanta tayi kasa sosai yanda baza a hango fuskanta ba kwata kwata, gashi ta duqa tana arranging plates da warmers din kan tray zata futa dashi, shiko ya dage ya bita da ido sosai at the same time gabanshi na faduwa ya rasa dalili.
Kallonshi nanna tayi ganin yana kallon inda sabeeha ke tsugunne, ga sabeehar itama bata dagoba kamar wadda ke tsoron za a kamata da wani abun”
“Fatima??…”
“Na’am” sabeeha ta amsa ta, ciki ciki “jeki kawai,”
Naam dinnan datace ne ya kara sashi kallon inda take don ya dauke idanunshi akanta,kamar wani mai nazari haka
Sabeeha ko nanna na ce mata ta tafi tayi saurin miqewa ta futa.
“Bari na zuba maka da kaina” nanna tayi magana don ganin yanda ya kalli sabeehar ya tabe baki kamar wanda ke kyan kyami yasa nanna tunanin ko ba kowa yakeson ya sa mashi abunci ba, itama don taga fatiman nada tsafta ne sosai yasa tace ta saka mashi, amma ganin irin kallon daya mata yasa tace fatiman kawai ta tafi.
Kallon dayama sabeeha ya gane itace take zuwa part dinshi tana gyarawa, shi gaba daya ya dauka she’s mute ashe tana magana, amma ko sau daya bata taba gaishesa ba kuma duk ma’aikatan gidan idan suka ganshi kamar su tsugunna mashi,
Sabeeha na fita daga dakin ta sauka kasa, itafa wannan abu ya fara damunta, kullum tsoro da fargabar haduwa dashi take, shiyasa take kokarin ganin ta raba hanyar dazai sadata dashi gaba daya, Har Allah allah take su koma school.
Zaune take bakin gado ta dora kafa daya kan daya tana sanye da irin camisole dinnan dake kama jiki sosai, hadiza na daga zaune bakin gado sai faman yaqe take yi.
“Hajiya karama dan Allah kiyi hkuri….”
Wani irin disgusting kallo maya ta mata tare da cewa “hkurin me kike bani?”
“Wai naga kwana biyu idan nazo gyara sai rabi tace kince karna sake zuwa bangarenki sainayi tunanin ko dan saboda abunda Fatima tayi ne”
“Meysa zan yarda dake? Yarki barauniya”
Murmushi hadiza tayi tace “laifin yata saiya shafeni?”
“Na tsaneku wallahi, dake da yarki, ko ganinku bana sonyi”
“Bakya son zamanta ne a gidan nan?”
Kai tsaye tace
“Eh..”
“Toh saina maida ta inda muka futo indai zamanta anan yana damunki”
Kallon mamaki maya kema hadiza, “akan farin cikinki ay zan iya komai kuma zan iya sadaukar da komai”
“Harda yarki?”
“Eyy wallahibki yarda dani,”
“Kina tunanin zan yarda dake ne?” Maya ta jefo mata tambaya, “hajiya karama kenan, nasan fa ba yarinyar nan ce ta dauki abunku ba ranar da kika shugo dakinmu aranar kika aje abunnan kuma na ganki da idona amma ban fadawa kowa ba saboda banason a bata maki ranki, yanxu zaki iya yarda da maganata”
From the shock on her face zaka gane cewa mamaki ne karara akan fuskanta, kallon hadiza kawai take abubuwa na circulating aranta.
Sai kawai maya tayi murmushi don babu abunda yazo ranta sai tunanin duk yanda akayi sabeeha yar kishiyar hadiza ce, uwarda ta haifeta dai bazatayi wannan abun ba amma ita meya dameta da wannan, she just wants to see the girl miserable don kawai akwai something off datake ji about yarinyar, wanda ke sata feeling anxious and scared kuma ta rasa dalili.
Chan bangaren jamila, dahiru fa baibar kiranta ba kuma taqi dagawa saida taga ya mata wani dogon text yasa tayi saurin kiranshi, yana dagawa tace “dahiru me kakeso?Ehh”
“Jamilaa..jamilaaaa ki daina qin daga wayata, wallahi kinsani babu kai, karkiga wai girma yazo wallahi cikakken dan tasha nake”
“Toh me kake so? Ehh?”
“Kuna tunanin zaku yagi arziki ku barni ko? Toh wallahi baku isa ba,”
“Me kake nufi kenan?”
Dariya ya kyakyace dashi yace, “naji ance yarmu ta girma, madallah ashe dai da rayowar imani aranku keda kawar taki,“
“Me kake so dahiru, ka daina kirana tun kafin jamilu ya gane”
“Toh toh..saurareni, tunda kunci moriya nima sai a barni nasha romo ko?”
“Me kenan?”
“Kinga shekara nawa kenan tunda kika gujeni banyi aure ba, kuma da kumari na wallahi, man power nake sha duk sati kuma abar tawa kullum bata kwanciya, shine nakeso ku bani yar tamu ko? Asirin namu yafi rufuwa dakyau ko ya kikace”
“Wai kana nufi hadiza ta baka yarta??”
“Ah ah ke kuwa yarta kuma? Kodai yar da kuka chanzo”
Dammm gaban jamila