Author : Queenmerh Category : Complete Novels
ya bada, wallahi karamin hauka ne dahiru bai sata ba, tashin hankali da ba a sa mashi rana.
“Kinga saimu rufawa juna asiri ko?” Ya karashe yana kyakyacewa da dariya.
Saurin danne abunda ke ranta tayi tunawa da babu abunda zai iyayi,“idan muka qi fa? Me ka isa kayi? Meka sani dahiru? Bakasan komai ba, barazanarka ta banza ce wallahi dahiru,mteww dan wahala”
Tana fadin haka ta kashe wayar, ta soma kiran hadiza, hadiza na dauka ta labarta mata komai wayar da sukayi da dahiru, hadiza tayi shiru tana wani nazari.
“Dake shi tsinannne wai tunanin yayi min barazana zaiyi, bayan babu abunda zai iya, kowa idan talauci ya gama bugunshi sai kuma hauka, kinyi shiru bakice komi ba?”
“Jamila…anya wannan ba shawara ce mai kyau ba eh? Zamanta anan yana kawo min matsala, na kasa jan yata a jiki, kuma farin cikinta shine damuwa ta ayanxu,”
“Yanxu me kika yanke kenan”
Dariya hadiza tayi tace “dahirun ne daman daidai da ita, ay namayi kokari rikon danayi mata shekara nawa?ki kirashi ki shaida mashi na bashi ita wallahi, zansan yanda zanyi da hajiya”
“Kice kawai dangin ubanta ne sukace lokaci yayi kuma an mata miji, ina wannan matsolon kanin dalha, ki bashi yan chanji kawai ki rufe bakin sa”
“Hakan ma za ayi, kinga kuma kwa huta da masu nemanta, inama zan bari tayi associating da masu kudi, kamar yanda kikace ne kila wani ya ganta yakeso shine yake bibiyarta ay bazan taba bari a sauya mata rayuwarta ba wallahi,ina ribar tawa kenan?”
“Oh hadiza kishiyarki ta shiga uku…”
“Ay kishiya daya gareni a duniya, ba a taba abunda hadiza ta kwallafa rai akai a zauna lafiya, wallahi zan iyayin komai jamilaa…”
“Haba waa dama chan kinyi sanyi ne hadiza yanxu nasan asalin hadiza ke magana, kinfi shaidan” suka kyakyace da dariya….
….
The next day..
Yau ta kasance Saturday’, da sassafe ya futa gym don ya saba da hakan yana dawowa gida lokacin wajen karfe tara saura, wayarshi ya dauka ya soma kiran salim, yana dagawa ya tambayeshi any update akan jamilu, ya shaida mahsi gar zuwa yanxu bai nemesa ba, taj yace anya kuwa ba guduwa yayi ba? Salim ya shaida mashi ay irin waennan mutanen idan har sukaji maganar kudi babu abunda baza su iyayi ba, haka nan sukayi sallama gaba daya ya kasa samun natsuwa, a matse yake da yasan inda take, shin ko tana cikin koshin lafiya? Wace rayuwa take yanxu? Tunawa da sanda ta bashi labarin ita marainiyace yayi, da kuka abubuwan datayi mashi, He wants to pay back for everything taht she did for him, she stood by him alokacin dayafi kowa buqata, ta kula dashi dukda tasan rayuwarta na cikin hadari.
Ta wani bangare na zuciyarsa kuwa begenta yake, kuma mararinta ganin ta yake,ta rigada ta kamashi sosai withouthis acknowledge,bai gama sanin cewa tabbas ta zama wani bangare na rayuwarsa ba saida ya koreta da kanshi, yanajin kamar he’s incomplete without her.
Sauke ajiyar zuciya yayi yana akan kujeran sitting room din, ya dan rufe idanunshi kamar maijin barci.
Kafin ya futa ya shiada ma nanna zai futa bazai samu yin breakfast ba, so kafin ta futa wani meeting za zatayi da wasu client dinta tasa rabi akai mashi breakfast.
Rabi ko babu wanda zata sa yakai breakfast din banda sabeeha tund aitake kula da bangaren nasa.
“Suna zqune a daki ita da basira, tana bude handout din da aka rarraba masu a school rabi ta shugo da sallama.
“Fatima zo kije kikai breakfast chan bangaren da kike aiki”
Tund ataji ance tazo takai tasan cewa yana nan, duk taoron da takeji haka ta danneshi ta tashi ta ambula hijabi wata davara ce tazo mata daman akwai wata doguwar riga da aka taba bata tanada kayafi baqi, daukan mayafin tayi ta fuce daga dakin,
Nufar part din tayi daidai nan maya data hangota ta balcony din hutawa na sama da aka kawatashi da greenish grass carpet ta sauko, waya takeyi fa da wani friend dinta amma tayi saurin katse wayar ta sauko kasan,
wajen bakin kofar ta tsaya ta nada mayafin a fuskanta tayi kamar niqab dashi kafin ta bude kofar tare da sallama.
Kafin maya ta iso harta shiga ciki,
Sabeeha na shiga ta hangoshi a zaune sitting room din tayi saurin sauke kanta kasa bata yarda ta sake kallon inda yake ba ta tunkari wajen dining ta ajiya abuncin.
Tana ajewa ta ko jerawa batayi ba juyo zata bar parlorn maya ta shigo cikin part din kamar an wullo ta.
Kallo daya tayi ma sabeeha dukda tana cikin nikab ta kalleshi yana daga zaune kawai wani irin kishinsa ya turnike ta.
Da sallamarta da motsin shugowarta duk akan
Kunenshi, saidai hankalinshi baya kanta kwata kwata, yadai san mutun ya shugo part din kuma ya gane koma waye, yarinyar dayyi tunanin shes mute, ashe she is not, the girl dayaji nanna ta kirata da fatima, wani rainin hankali ko sau dari zata wuce ta gabanshi bazata taba bude baki ba tayi magana, very disrespectful, bawai yana bama starngers attention ba ko ya damu kawai dai rainin hankalin yarinyar nan ne ya tsaya mashi arai baima san sanda yasa abun aranshi ba kodan yaji ranar an kirata da fatima ne? Kuma ta tuna mashi da mai sunan.
“Ubanwa yace ki shugo da kazamin jikinki nan bangaren?”
Sabeeha banza tayi da ita don bata da lokacin wannan allah allah kawai take ta futa, A daidai lokacin ya bude idanunshi.
“Fatima…!” Ya kira sunanta anatse
Itako hawan ruwa ne batayi ba, ta tsaya chak kana ganinta kaga mara gaskia gaba dayanta,
“Fix the meal?” Ya fada yana miqewa tsaye bai kalli inda suke ba ko ya basu attention, maya tayi saurin cewa
“Good morning uncle, can i do that instead?”
“Let her do her job” ya bata amsa yana wucewa sama, hes so cold towards maya ko me yasa? Ita kanta she keeps wondering haka, amma yanxu kuwa daya kira sabeeha da sunanta sannan a gabanta yace sabeeha ce zata zuba mashi abunci ay kawai sai maya taji kamar an taru an watsa mata garwa.
Idanunta sunyi jaa sosai ta dubi sabeeha cikin idanunta sabeeha ko ta kalli cikin idanunta tana hango tsoro da fargaba ko ba a fada mata ba tana ganin yanayin maya tasan cewa she’s jealous, ana wata ga wata.
A fusace ta futa daga part din kamar zata tashi sama.
Sabeeha tayi kwafa tace “matsalarki ke daya mtew”Tana gama abunda take ta futa.
Jamila ta kira dahiru ta shaida mashi yanda sukayi da hadiza, kamar ya zuba ruwa a kasa ya sha,harda godiyar munafurci, aranshi ko tunanin da yake da abunda yake kullawa shi kadai yasani, jamila ta gama raina mashi hankali batasan cewa ya fita tashanci ba.
Hadizq ko ta nemi kanin dalha tsohon mijinta rabonda ta nemesu tun bayan mutuwar dalha da sukazo daukan sabeeha tace basu isaba ba suka barta da yarta, ta shaida mashi komai da hukuncin data yanke, bashida jaa akai kuma bazaiqi shiga lamarin ba don yar dan uwansa ne wannan yasa yace toh shiknan.
Dahiru yayi yayi yazo ya ga sabeehar jamila tace bai isa ba, kawai dai ya jinkirta za a nemeshi, da yan kudadensa a jiki ya soma shirye shirye.
Washe gari da safe hadiza ta shiada ma rabi tanason ta samu hajiya anne, akwai maganar data taso tanaso ta fada mata, rabi ta mata iso wajen anne tajw don ta shaida mata, tana zuwa ta soma mata bayanin kanin mahaifin sabeeha ne yace ya mata miji, kuma lokaci yayi daya kamata ayi mata aure.
Anne najin wannan magana ta nunfasa, ta tambayi hadiza ita ta amince ne da batun nasu tace mata eh ta amince.
Na farko dai anne tayi mamakin yarjewar hadiza don kowacce uwa zata so taga yayan ta sun samu ilimi wanda zai taimakesu koda bayan sunyi aure, daga yanda ta amince lokaci gida anne tayi sensing kamar hadiza bata damu da karatun yar tata ba.
Gashi yarinya mai hazaqa da basira, kuma ga dukkan alamunda yanda hamad ke fada mata yarinyar nada interest akan karatu kuma tanada kwakwalwa don duk tafi su laila nesa ba kusa ba dukda ita ce tazo a bayansu.
Tambayarta anne tayi ko yarinyar ta amince, hadiza tace ay bata fada mata ba.
“Toh ay kamata yaui ki tambayeta, we’re on the 20th century hadiza an daina auren dole a wannan zamani in khma karatu take sonyi fa?”
Anne ta tanbayeta hadiza tayi shuru, “ni zan tambayi yari yar dakaina naji idan karatu takeso saidai ki basu hakuri, hadiza dai kasa cewa qala tayi daga decision din anne, yanda kasan an rufe mata baki ruf kodan tana shakkar anne ne ko kuma don tana mata kwatjini ne allahu a a lam, ita da yarta amma tana jin kamar an fita iko akanta.
•••
Tunda Salim ya kirashi ya shaida mashi cewa jamilu ya kirasa ya kasa zaune ya kasa tsaye, ya aje duk wani abunda yake ya futa, yana isowa inda zasu hadu da salim ya tadda har ya dauko jamilu, zuciyanshi wani irin harbawa yake kawai so yake ya ganta.
Taj na karasowa ko tsaywa gaisawa ma baiyi ba ya dubi salim yace “has he found anything?”
‘Murmushi salim yayi yace “yes sir, he will be taking us where she is”
Wata nauyayyiyar ajiyar zuciya mai dauke da relief ya sauke ya dubi salim yace “what are we waiting for????”
“Sir calm down, he wanted to be paid before…”
“Ka tura mashi 2m” zato ido salim yayi, ya kara jaddada mahimmacin wannan yarinyar a wajen wannan balaraben mai danyen kudi.
“Okay sir”
Jamilu dai kallonsu kawai yake kan babu arabi babu boko, salim yace “idan ka kaimu har inda take yace a baka miliyan daya”
Jamilu ya wage baki yace “yanxu kuwa”
Suka shiga mota a tare sai maitamaaa…..💃🏻
“Innalillahi wa inna ialaihi rajiun” sabeeha ta furta tare da saurin rarrafawa wajen da anne ta yanke jiki ta fadi, kanta ya bugu da gefen center table “hajiyaa…hajiya….” Sabeeha tayi magana tare da dago kan anne da jini ya soma malala, hannunta na karkarwa ta kidime ganin jinin duk yabi hannunta, gashi anne bata nunfashi kwata kwata, cikin abunda baifi sakam biyu ba sabeeha na daga zaune bayan rabi tace hajiya na kiranta ta hau saman rabi kuma bata dade da sauka ba kafin anne ta futo ta zauna, tana futowa ta gyara zamanta zata bude baki kenan ta gaishe da anne kawai annen ta yanke jiki ta fadi, a guje sabeeha ta futo daga bangaren anne, jikinta na tsuma sosai ga jini nan a hannunta ta tunkari stair “anty rabii…anty rabii….”
Ta soma kiran rabi, a daidai nan maya ta futo daga bedrrom dinta kunnenta maqale da apple headset tana jin kida, ganin yanda sabeehar ta futo a rikice ga jini a hannunta yasa ta cire abun kunenta.
Daga nan sama tana jiyo muryar sabeeha dake cracking tana kuka “ku taimaka… hajiya ta fadi..ta fadi…”
Maya najin haka ta shiga part din anne da sabeehar ta futo, ta ganta kwance ga jini na bin fuskanta, ay batasan sanda ta kwala kara ba jikinta na bari, daidai nan rabi da sabeehar suka hau sama sabeeha kamar za a zare mata rai hadiza ma ta hauro saman.
Hannu aka rabi ta dauka ta taho a guje kamar zatayi supa ta tsugunna gaban anne ta tallabo kanta “innalillahi wa inna ialaihi rajiun hajiya??? Hajiyaa?????meya sameki hajiya? Na shiga uku ni rabi,basira yi gudu kije bangaren hajiya fadila ki kira ta, ko hamad ki sauri”
Maya dake cikin shock din ganin anne ta kalli sabeeha dake ta faman yin kuka.
Wayar dake rabi dake jikinta tayi saurin lalubowa ta kira nanna, wajen sau biyu tana kira ba a dauka ba ta soma kiran ya sameer, shika bai dauka ba, gaba daya kowa sai kuka, musamman sabeeha harma da rabin, hadiza ko gizau, maya kam ta tsaya tana kallon sabeeha allah kadai yasan me take kissawa.
Basira na zuwa ta shaidawa anti fadila ta fito da gagagwa ko mayafi bata saka ba, hamad da laila basa gidan ta tura su zumunci gidan uncle dinsu kanin mahaifinsu.
Fadila na haurowa saman jiki na bari ta taho da gudu wajen anne, “innalillahi wa inna ialaihi rajiun, meya faru??? Meya sameta???” Fadila ta fada ta karfi cikin tsoro da fargaba da tashin hankali, ga anne dai a kwance bata motsi bata nunfashi.
“Na shiga uku ni fadila…”ta tallabo kan anne ta dora kan cinyanta jini duk ya bata mata hannu utama, ay jini. Data gani ne yafi kidima ta.
Sabeeha dake tsaye tana hawaye Batayi auni ba kawai taji maya ta turata jikin bango idanunta yayi jaa sosai ta fara wani kukan munafurci, “me kikayi???? Me kikayii ma anne?????? Kece kika futo daga dakin, ga hannunki nan duk jini what have you done???”
Hadiza na ganin maya na kukan munafurci itama ta fara, “na shiga uku ni hadiza”
Kota kansu anty fadila batabi ba bataji bata gani tsabar tashin hankali ta kalli rabi tana hawaye tace, “taimaka min rabi”
Suka cicibeta harda hadiza, suka sauko kasa da ita, gaba daya.
Sabeeha nata kuka baiwar allah kamar ranta zai futa abun tausayi.
Wayar rabi na hannun basira nanna ta kira back, daukan wayar basira tayi, “hajiya..hajiya babba ta fadi, bata nunfashi”
“Rabi me kike cewa? Meya faru? Ki nutsu kimin bayani”
“Hajiya bamusan meya faru ba, mun shigo mun tafdata cikin jini, babu kowa a gidan”
Gaban nanna ya fadi take taji hawan jininta ya motsa, “innalilillahi wa inna ilaihi rajiun, sameer baya nan, tajudeen fa? Ku kaita asibiti ku kira ambulance”
“Hajiya duk basan nan?Amma ga anty fadila nan”
“
Kit nanna ta kashe wayar ta soma dialing number taj.
Su taj ko suna shawo corner layin estate din ya kasa cewa komai tsabar shock, baidai ce komai ba jamilu nata jawabin hanya, daidai lokacin nanna ta kira wayar, ya dauka.
“Tajudeen…kana ina? Anne ta fadi, sunce bata nunfashi, innalillahi wa inna ialaihi rajiun, karna rasa yar uwata”
Tana magana tana kuka sosai ba kadan ba, ai yafi kowa faduwar gaba da jin wannan zance shida yasan condition dinta.
Tuni ya kashe wayar ya dubi salim yace “speed up please kayi dropping dina a gida lets do this some other time, its emergency please”
Da gudun gaske salim ya karama motar speed har gaban estate din, jamilu yace “kai yallabai ay nanne esitati din, anan suke wallahi ita da babarta ance aikatau sukeyi”
Gaba daya hankalin taj baya ga jikinshi, amma dukda haka yayi mamakin maganar jamilu, yama kasa cewa komai, wayar nanna ta sake shugowa ya dauka, “oummi ki kwnatar da hankalinki babu abunda zai sameta gani nan ina cikin estates,babu abunda zai sameta” yayi magana da larabci, jamilu dai sai rarraba ido yake, bai taba shugowa cikin gidaje haka hadaddu ba, gaban gaban mansion din satura’kis suka saukeshi suka juya, security suka bude ma taj kofa da gaggawa ganin yanayinsa.
Adaidai lokacin gaba daya suka futo hankali a tashe, yana hango anne a bayan fadila yayi gaggawar karasowa wajen jikinsa na bari yace “meya sameta? Meya faru da ita how and when did this happen? This can risk her life”
Fadila na kuka tace “bamu sani ba sunce faduwa tayi”
Maya data samu chance din magana ita bama ta tashin hankali da ake ciki take ba blaming game kawai take shirin yi,
“Wallahi itace, itace ta futo da jini a hannunta daga dakin part din anne”
.
Tayi nuni ga sabeeha yayi saurin maido da dubanshi ga sabeehaaaar…
Damm Gabansa ya fadi kamar zuciyansa zai fito yanda heart beat dinshi ke bugawa.
Baiwar allah Sabeeha sharf tama manta da wani batun yar buya da takeyi dashi, gaba daya a tsorace take,rabon da taga abun tashin hankali kamar wannan tun lokacin da take saudi.
Ahankali ya furta fatima….. gaba daya ya rikide ya sauya, abu biyu sun taron mashi, ga fargabar anne ga kuma fatima dayake ta nema a gabanshi.
After 3 hours..
Gaba daya daga kan sameer nanna taj da su hamad kowa gaba daya rankata kaf family din sun iso asibitin sun cika emergency ward, gaba dayansu, nanna nata addua charbi a hannunta fadila ko kuka take sosai laila tana tausasa ta, taj ko ya kasa tsayuwa shida yasan komai.
Futowar doctor barau yasa duk suka miqe nanna da idanunta suka kankance tayi saurin yin magana “doctor meke damunta? Meya sameta?is she okay?”
Shuru barau yayi yama rasa me zaice masu, ya dubi taj yace “i think its about time daya kamata su sani”
Nanna ta dubeshi tace “what are yiu talking about”
“Hajiya nada brain tumor”
“Whatttt!!!!!”
“Innalillahi wa inna ialaihi rajiun” kow aya fara yi
“Bataso a fadama kowa ba, taj was the only person that knew about this,kuma ta nemi alfarmar kar a fada ma kowa kar hankalinku yabtashi”
“Doctor…tell me she will
Be fine?”
Nanna tayi magana, sameer yace “how bad is it?”
“Shes on her treatment, idan har jikinta bai karba treatment dinba dole saidai ayi mata surgery a cire, yanxu its just a minor attack ta samu for now, thankfully bai taba brain dinba completely don zan iya cewa yana saka mutun ya zama paralyze”
Gaba daya suake ajiyar zuciya sukayi, doctor yace an kaita recovery room for now sannan dole ta zauna asibiti saboda a dunga tracking improvement na treatment din har sai an gama.
Godiya suka mashi gaba daya suka dunguma recovery, basu samu damar shiga ba suka tsaya bakim kofa suna hangota an saka mata oxygen.
Taj na zaune nanna tazo ta dafa ganin duk ya shiga damuwa sosai ba kadan ba, dazu da suka shigo da ita an dauka an rasata gaba daya.
Dafashi tayi tace “Meysa baka fadamin ba? Meysa ka boyemin?”
“Im sorry oummi, i had to, she will
Be fine i promise insha allah, she’s a strong woman”
Murmuahi nanna ta mashi tace “muyi ta mata addua”
Tunda anne tayi regaining conscious tuannin sabeeha ya dawo mashi, he actually saw fatima? Daman jamilu yace estate dinne, those that mean daman tana gidan all this while bai sani ba? Amma how? Kwata kwata bai kawo utace yarinyar dake mashi aiki ba don yanxu ne yake ganiyar tunani.
Yama rasa wani karatu zuciyarshi ke rerawa, he’s so shocked and so amazed at the same time.
Karshe dai kasa hakura yayi da zaman asibitin ya lallaba ya futa.
Bolt ya kira yana isowa ya hau ya wuce gida bayan ya kira salim akan cewa ya kawo mashi motanshi gida.
Yana isowa har wani mazari mazari jikinsa keyi, yana son kara tabbatar da bibi ya gani a gidan nan, bibim shi.
Babu kowa a kasan ko’ina shuru, tunawa da abunda jamilu ya fada kafin su karaso estate din ya sashi nufar kitchen, d more yana tunkarar wajen the more gabanshi