Author : Zainab Idris Makawa Seenabu Category : Complete Novels
mu gausuwa mukazo maku ba tsiya yakawo mu ba nan.
Mun fita muna jin su suna zage zage nace a raina ai in sakwatawa kuke kun hadu da
mama da hjya kubura a raina.
Bamu dadeba su baba sukace mu fito nan maji ke fadawa mahaifiyar shi cewa za a
aiko da kayan lefen da yai min.
Ko yanzu don anzo gaisuwane yasa ba,a zo dashi ba.
Matan sukace haba haba habadai da zafi haka.
Sai mahaifiyar shi tace wanan ai kyautane tsakanin ta dashi tun yana da rai don
haka mun yafe mata ba namu bane rabontane daga gare shi.
Allah ya bata miji nagari idan antashi auren ta a fada muna kada zumunci ya yanke.
Uwargidan Kabir da zamu tafi tayi kuka sosai muka rike juna tana min addua tace
zata dinga bugo min waya.
ZAINAB IDRIS MAKAWA
SEENABU
IDAN BAKI BIYA BA KADA KI KARANTA HAKKIN WASU PLEASE,,,,
I DAN KIN TURAWA WA WANDA BAI BIYA BA MU YAFE MAKI BA ALLAH YA ISAR MUNA A KAN KI
Bayan mun dawo gida sokoto babu abinda mama keyi sai lalashi na tana kokarin taga
na saki jikina sosai.
Amma na,kasa sakin jiki saboda shakuwa ba karamin abune ba ga dan adam.
Na kasa cire Kabir a raina gaba daya ko yaushe zaka ganni nayi zaune nai shiru ni
kadai ko idan ana hira ni na zauna naita tunane ni kadai.
Yau ma zaune nake saman dogon kujeran falon sai hira suke a tsakanin su akan Ahmad
dan wurin mama Asiya.
A zahiri kallon su da sauraren su nakeyi amma zuciya na tai nisa da inda suke
zaune.
Sai da naji murya mama cikin fada tana magana ko shi sai da Maryam ta dan taboni
na,zabura firgigit dani.
Yaya Sadauki na gani tsaye cikin kaya bakake sai kwalan rigan ke da jan kwalla
daga saman shi, kamshi na tashi daga jikin shi.
Kallon mamaki yake min irin yadda na koma a lokaci daya na koma Bintu shiru shiru
dani ban magana kamar ba nice ba.
A hankali ya tako zuwa inda nake zaune saman kujera na takure kaina guri daya ina
makure kamar mai jintsoro.
Zama yayi daga gefen kujeran da nake zaune na dago ido in kallon shi a cikin
mamaki don, bai taba zama haka a kusa dani ba.
Yace, Fatima har yanzu baki sake jikin ki ba ko kin fi son ki tayarwa maman ki da
hankalinta ne,?
Na ce tare da girgiza kaina da,a,a, yace may yasa bazaki hakkura da ikon Allah ba
Fatima.
A hankali na sa gefen hannun na ta baya na,share fuskana yake tabayan kinci
abinci kuwa?
Kafin na bashi ansa sai muryan maryam tace maryam bata cin komai da koko sai dan
ruwan liptop da take sha .
Ya mike yana cewa kina,son ke ma ki kashe kanki ke nan kibi Kabir din ko ?.
Yakareshe zancen tare da mikewa ya,bar dakin a lokacin don dama fita zaiyi.
Na dan na dan fara sake jiki saboda irin matsin da suke min gaba dayan su a part
din mu.
Tun dai mama wani lokaci sai ta nuna min bacin ran ta karara a,fili nakan shiga
taitayina na kama kaina.
Gaba daya nakan ji komai bai min dadi nakaji zuciyar ta a bushe komai ban so ban
ra,ayi ko kadan.
Idan suna hira ko yar dariya sai naga basu damu ba ko don basu akaiwa mutuwar bace
abin bai damay su ba hakanan kaman yadda yake damuna ako yaushe.
Yadda Sadauki yake kokarin nuna min kulawan shi na yan uwantaka tankar ciki daya
muka fito dashi.
Shidai tausayi ma nake bashi yanzu don yasan mutuwa abune mai cin zuciya sosai
kafin ya fita.
Ina mamaki ni kaina yanzu ko bai ganni ba sai yace a kirani idan nazo zaice
kinci abinci ko ?
Nakan bashi amsa da eh ko a,a sai yace a dauko naci a gaban shi mama tana jin
dadin yadda yake matukar nuna min kulawanshi sosai akan abinda ya samay ni.
Da zai tafi sai da ya kara yi min nasiha sosai yace kuma idan yatafi yaji ance
ina wani abinda bai dace ba zai zo da kan shi ya dauki mataki.
Nace a hankali insha Allahu yaya bazanyi komai ba ai na hakkura insha Allahu.
Yace da yafi maki don kin san halina dai zan iya maki abinda nace din.
Da zai tafi hardani muka rakashi bakin motan da Bashar zaikaishi airport har ya
zauna nakecewa a hankali yanzu Anty maryam shima yaya jirgin zai shiga ne ?
May waccan take fadind wai ?
Yana tambayan maryam.
Dariya take tana fada masu abinda nace nikan fuskewa nayi kawai.
Yace ko na fasa na shiga mota kada nima na mutu ko?
Bashar yace Fatima ai da motan da jirgin ko basu idan kwanan mutum.ya kare mutuwa
zaiyi.
Sadauki yace kasan bakauya ce ta dauka jirgine kawai ke kashe mutane.
Har motar ta daga yace ke zo nan .
A hankali na isa inda yake zaune yace kin dai ji abinda na fada maki ko?
Nace eh yace kwana nawa wani tsohon zai bullo maki idan kinyi hakkuri don haka
bana son naji kin kara somay wa maji a daki kuma.
Dariya akasa suka, wanda nima dariya abin ya bani har fararen hakorana suka dan
fito yace to ke fa kullun kina cikin shawa mutane toka agida waike tsofo ya tafi ya
barki.
Suna bacewa, daga layin Bashar ya sauke ajiyan zuciya yace, wallahi tausayi
yarinyar ke bani Allah.
Yace akwai tausayi shiya nake kokarin gani she feel free don kada abin yai mata
illa gata karamar yarinya.
Amma gaskiya ya kamata fa asan abinyi anan man don wallahi ni dai ina maka
kwadayin wanan yarinyar Allah ko.
Kai Bassh kada kaja min raini please kaunata ce fa don Allah bari kada ta raina
ni.
May ye abin raini anan kuma aure ne fa kasan lokacin da zaka lume ciki kana I
love you baby, I miss you,
Wallahi kadai dan iska ne ga,wanan yar yarinyar bakauya zan tsaya ina wanan
shirmayn haka sai kace wani soko can.
Dariya Bashar yayi yace kanace wasa nake yi to gwada kagani in baka samu kan ka
ga stage din nan ba.
Jeka gwada kai da baka,san kunya ba yace nikan anan ban sani ba gaskiya sai ma ka
dawo zaka gane ban sani ba ai don zaka samay ni dumu dumu wallahi.
Agurin wanan yarinyar ko a ina ai ita takace da ka ganin gurin tunima,
A wani gurin dai da nake shirin shiga very soon.
Don akawar da zancen ya jefo mai zancen kasuwancin su da haka suka isa airport
din.
Sannu sannu na,fara sakewa na far normal life dina kaman yadda na,saba a baya,
can.
Sai kuma na dan fahinci ashe na dan saba da yaya sadauki kwana biyu ban sani ba.
Sai yanzu da baya gari na fahinci muna kewan rashin shi agida abinda bantaba ji
ba idan bai nan a rayuwana.
Saidai nasan kila dan kulawan da yake bani ne kwana biyu yadan ja muna shakuwa
tsakanin mu.
****** ********* ******
Bayan kaman wata uku da rasuwan Kabir ba laifi gaskiya don zuwa yanzu na dan sake
sosai na rage yawan damuwan nan da nakeyi.
Shima acan idan yai waya yakan ce abani mu gaisa kamar yadda yakan gaisa dasu
Amirah.
Sai dai ni ba wani dogon magana ne mukanyi dashi ba yakan dai tambaye ni yaya
karatu ya kuma gida.
Sai dai idan mun gama,waya kamar yadda nakan ji shima din haka yakanji a ranshi
sai dai kosan mu yana daukan haka a zumunci ne kawai.
Yadda bai taba jin yana sona ba nima haka kowan mu dai yana son dan uwa na yan
uwantaka ne kawai ba wai wani so ba can.
Yau saye nake cikin dogon riga din kin kasar Dubai da mayafin rigar ne na yafa a
kaina ya dan rufe min har rabin fuskana kadan.
Na samu mama a,falo nake gaishe ta, ganin yadda nai kwalliya haka yai yasa mama
tambayana yau kuma,sai ina haka Fatima?
Na ce cikin dan sakin fuska tau gani nan dai mama gidan su maman arkilla nake son
zuwa nagaida ita.
Cikin mama Maji take cewa yau din ashe hjy tayi sa,a yau ranan nata ne nace Anty
maryam ki daure mu tafi please ?
Tace na,fada maki ban zuwa gidan nan sai lokacin da zuwan yazo min a,rai zan
tafi.
Banyi fushi ba sai murmushin da nayi ina fadin ya kamata ace ki daure mu rafi tare
yafi min zuwa ni kadai.
Ranan da na tafi aini kadai na tafi kemay may kika hana kan ki rakani.
Nima yau Allah ya ban sa,an ki sosai wallahi, haka naiwa su mama sallama na tafi
gidan,
Na dan dade a,saman titi kafin na,samu abin hawa sai ga wata,mota tazo wucewa tin
daga nisa na gane cewa mace ce ke tuka motar a lokacin.
Naso na,sheda su amma sai na,rasa gane a ina na,san su ne ma abin ya, shige min
a,rai.
Kwanan zuwa gidan mu suka nufa, suna shigewa ina samun mota na shige abina.
Maman su Bashar tayi murna kwarai da,ta gannin don bata tsanmaci zuwana ba.
Nace na shigo na gaida ita,na kuma yi mata kokarin da,tai min da,rasuwan Kabir di
na.
Da hanzari tace kai Fatima kin taba ganin don iyayye sun wa dan su abu yace yazo
godiya, nakai wani dan lokaci tana ta m8n nasiha a cikin hiran na mu wanda shi yafi
yawa.
Nai mata sallama na kama hanyan sai gida ina,shiga na samu anyi dandali a tsakar
gida.
Nace wai yau sa idawannan kuma nan aka baje ne ina gaishe su na juya,sai cikin
shiyan mu bankai ga shigewa ba naji ana fadin a haye duniya tai masu dadi an mutu
anbar mata kaya sai shiga da fice takeyi a cikin su.
Maji na ganina take cewa a,a shin har andawo ne wai yanzun fa kika fita Fatima.
Murmushi nayi raina a bace mama tace may kuma akayine wai naga kin futa cikin
dadin rai gashi kin dawo muna a murde kuma.
Nace cikin hawaye mama kinji abinda umma take fada min wai duniya tai min zafi an
mutu anbar min gadon kayan lefe sai yadda naga dama.
Tace kai Fatima ki barta mana tunda ta zama tsohuwar banza kamar ki zata tsaya
kuma ta yadawa magana haka?
Ina ruwanta da ke da har wanan irin zancen zai rika shiga tsakanin ku da ita
kuma?
Amira dake fitowa tana ji tace halin su ne kawai na bakin ciki da hassada irin
nasu, da yarta ce ai baka jin zamcen komai akan ta.
Amma tunda zance ya kawo nan shine abin bakin ciki kuma, bamu san lokacin da yar
iya tafita ba tana cewa to ai in wanan rigunan ne na jikin Bintu duk muna dashi
harda Siyaman mummy a sayowa irin shi ba cikin kayan mamacin bane ta saka.
Umma ta fahinci maganan Maryam daga inda suke zaune take cewa kai shi yaro idan
baida kunya bai tsoron uban kowa walleh.
Ku daiyi tayi ai anan zaku tsufa dakin uwar ku kuna taya ta kishi ko kare bai
zuwa sunsuna inda kuke.
Sai kyashi da hassada in kunga yan uwa sun samu sabbin samari idon ku na sama sai
kun yi kitihin da kuka rabasu dasu.
Yan banza masu abin fadi waike mara kunya kinzo mayar muna da martani ko ke da
baki da kunya.
Ni ko mashayin yayan ku bai isheni ba wallahi balle ke abin banza har gobe dai ba
mai abin ashha kamar ku a gidan nan, mutane kawai marasa mutinci.
Karan buga kofan shigowa gidan da,akayi da karfi shiya mayar da hankalin su gaba
daya ga mai shigowa gidan.
Wasu matane su uku tallabe da,wata yar yarinya dul jikin ta jini ne tako ina
kaman an yaka rago cikin tashin hankali suke fadin ina mahaifiyar,
Imirah gidan nan ?
gaba daya hankalin kowa ya koma,gare su matar sai kuka take da yarinyar tallabe
a hannun ta.
Kafin wani yai maga saiga "yassanda mace ta shigo tana fadin waye uwar imiranah
gidan nan?
Da sauri maryam tace kufito ga yan sanda a gidan mu wai ana neman uwar imiranah.
Hajiya kubura shigowan ta ke nan tun a kofan gida taga mutane dafifi take
tambaya wani makwabcin su ke fada mata wai anzo kama Imiranah ne,
Tana shigowa takai ido akan yarinyar dake kwance jina jina hannun iyayyen ta
Tace innalillahi wa yai mata fyade kuka shigo muna da ita gida haka ne?
Yar sandan tace wani a gidan nan something Imiranah ko waye shine wai tun da
safe da yarinyar tafito tallan kunu ya jata yana lalata da ita shine yai mata wanan
aikin haka.
Salati muka saka gaba daya manya da yara umma ko duk karfin halinta yau sai gata
tana kuka ta,shige daki.
Hjy kubura itace ta kira Alhaji tazo gida ya iske wanan tashin hankalin mai muni
a gidan shi.
Ga matasan unguwa su yi dafifi a kofan gidan sunce sai an fito masu da Imirah ko
su bankawa gida wuta don ya ishe su a cikin shiya da dannan masu yara.
Ranan munga tashin hankali mugan fitina a filin Allah don ga matasa na bugun gida
sai an fito masu dashi wallahi.
Sai da Baba ya dawo shida kan shi yaba da umurnin a shigo a duba ko ina sako da
lungun na gidan shi ko an boye shi idan za,a ganshi.
Ashe yana daga bayan dakin maji yan sandan nashiga suna fita maji ta gan shi
cikin dubara ta jefa mai hijjab ya sa yaboye fuskan shi ya zo shigowa dakin mu na
ganshi zanyi magana maji tai min signal da ido nai shiru, batare da wani ya gan shi
ba yashige ciki,
Allah yasa wani ba wanda ya gane shi har yashige ciki, don anyi yawa sosai wani
baigane wani a gidan saboda cika ga hijjib din babbane har kasa yake.
Can ta kaishi ban dakin ta ta boyeshi ta dawo waje ana taneman duniya ba a gan
shi ba a gidan.
Akace tunda bai nan ya gudu sai dai a kama baban shi ko mahaifiyar shi,
Nan wani sabon fitina ya tashi a lokacin ne maji taji kaman ta fito da Imiranah
duk da tasan ranan matasa na iya kashe shi yadda suke wanan ihu da ashar akan afito
da Imirana din.
Baba yarinyar da akaiwa fyade yafara fadin idan na bari aka tafi da Alhaji ban
kyauta mashi ba, irin yadda suke muna kokari a unguwan nan shi da dan shi Umar
Faruk Sadauki.
Bani ba duk wani magidanci a uguwa nan yasan irin mutuncin da sukewa mutane don
haka ni ba Alhaji ko matar shi ce tai min laifi ba dan shi Imirana ne kuma shine
nai kara gurin hukuma ya bata min yarinya.
Mutanen gurin suka ce gaskiya kayi kokari kayi gaskiya a bari har aga shi macucin
babu ruwan Alhaji don bai aike shi ba.
Nan Baba yake cewa ya kamata a taimaki yarinyar a tafi da ita asibiti kada tazo
ta mutu saboda jinnin dake mata zuba yai yawa sosai.
Fita da yarinyar shine dalilin da yasa mutane suka,kwasa,aka fita daga gidan tare
dasu Alhaji akatafi asibitin.
Masu kuka nayi masu bata fuska nayi da yaudai kan yau ne don dara taci gida
zancen kiran wasu yan iska ya kare a gidan nan don ashe kowa nada dan iska har da
tantirai a dakin shi.
Hjy Kubura ce take fadin haka yayin da take tafiya zuwa part din Alhaji ta nacewa
yau yadda akai tonon asiri da fallasan da yakai wanan cin mutuncin da akai muna
kato har cikin makewayin mu don wani katon mazinaci.
Mu kan yau wallahi ancuce mu gidan nan wanan cin fuskan da may yai kama aiko
munga iyakan iskanci a gidan nan .
Umma na ciki tana jin ta amma ta kasa magana don yau baki ya mutu murus.
Ga tashin hankali tasan yai Imirana sai Allah sai Allah Allah takeyi kada a
ganshi a kashe shi.
****** ********* ******
Maji saida taga an watse ta shiga dakin ta ta bude bayi tace mai yafito yace
cikin rawan murya wallahi maji idan nafito kashe ni zasuyi.
Tace nace kafito muyi maga duk sun fita don ba waje zan fitar da kai ba ai.
Yafito duk jikin shi rawa yakeyi ta zauna bakin gadon ta shikuma ya zube a kasa
sharkaf ya dukar da kan shi kasa.
Tace Alhaji karami yaya akayi kai wanan aika,aikan haka wa yar karamar yarinyar
nan.
Shiru yayi tace gaskiya baka kyautawa kan kaba kuma baka kyautawa iyayyen ka ba.
Mutum yana barin abin fadi kodan bayan shi da mutuncin gidan su.
Yace cikin sauke ajiyan zuciya wallahi maji sherin shedan ne kawai amma ayi
hakkuri tace yanzu wanan abin ni ban san yadda za,ayi ba ma wallahi.
Tace gashi dan uwanka baya gari shikuma Ahmad nasan kona fada mai kana nan zai
iya fallasaka asani.
Tace amma ka zauna anan har dare yayi mugani don kada ka fito ko fallo ne a san
kana nan.
Ta mike zata fita sai kuma ta juyo tana tambayan shi da cewa kaci abinci ma kuwa?
Yace maji ban iya cin komai ma wallahi don gaba daya ban san yadda akayi nai wanan
abin ba.
Maji tace bari nazo sai tafita daga dakin muna falo tace Amirah hadowa yayan ki
tea mai kauri ya sha.
Da sauri suka juyo suna kallon ta da mamaki azaton su ko ta rude ne tace wa
Amirah tashi mana ki hado mashi.
Tace wani yayan mu Maji ?
Tace Imiranah mana.
Yana ina maji ke ban son tambayan tsiya kuma ku kama bakin ku wallahi.
Baba basu dawo ba sai guraren sha dayan dare yazo ya shiga dayake girkin Hjy
Kubura ne bai dade ba suka rufe kofa don cikin tashin hankali yake.
A lokacin da mama taji sun rufe kofa tasaka hijjab