Author : Zainab Idris Makawa Seenabu Category : Complete Novels
shan dumin junan namu ne yake cewa cikin
wata irin shakkakiyar murya su waye nagani a falo kuma a ina suka fito hakane da
au kuma ?
Nai dan murmushi tare da dan dago kaina daga jikin shi nace ban san da ga ina
suke ma amma kullun dasu muke wuni a gidan nan sai dai na girka na basu idan kuma
sun gama na kwashe na gyara gida idan da duk ya baci.
Yace a bisa ga umurnin wa hakan ke faruwa min a gida ban sani ba nace umurnin
second command ne Anty Amira don haka sai ka tambaye ta bayanin komai.
Ina rike a hannun shi yaja hannuna zuwa falon muna shiga suna ganin mu suka sauri
dawo da hankalin su a gare mu irin yadda suka gan mu a tafe ne ya kara daure masu
kan su.
Zama mukayi a saman kujera daya nidashi ya dago fuskan shi dake a daure yana
fadin wa yan nan kuma fa daga ina suke ne haka ?
Shiru babu wanda ya amsa ya dago kan ahi yana kallon inda nake yake yana cewa
nace su wayen haka kuma don ban san su ba.
Nace ka tambayi anty Amira don tare na gan su dasu kuma ta fada min sunfini
daraja a gidan nan kaga ni dole sai dai na bisu don yan uwankane na ji aiko.
Sai dana fadi haka ya dago kai ya kalli inda Amira take zaune wani irin haushin
ta ne da kiyayyan ta ya darsu a zuciyar shi a lokaci guda.
Yace su waye haka kika tara min a gidana sai cewa tayi yaya sadauki salma ce fa
diyar gidan baba prof da take mutuwan son ka wace nasha fada maka zancen ta tana
karatu a london yanzu itama tagama ne ta dawo gida.
Wani mugun kallo ne ya watso mata yace kina da hankali kuwa Amira look kwashe min
wanan mugun tarkacen da kika tara min a gida don yanzu na gama sanin inda kika
dosa.
Salma da ta zage akan ta aamu shiga tunda ta samu kaunar shi nason ta sai yadda
tayi dasu.
Dalilin ma da aka kitsa ke nan su dinga zuwa gidan don ta san halina da kuma
yadda zata saba da gidan kafin ta shigo.
Haba UF inji salma data mike tsaye tace kaima kasan da ina son ka shi yasa kaga
har nazo gidan ka kawai .
Amma daba, son ka nakeyi mai zai kawo ni wanan nan gidan nazo na zauna har wanan
yar matsiyatan daka aje tace zata kawo muna raini kawai.
Don mun sauki cups din amfanin ka ta kama muna haushi ai badon Amira da ta dauki
mataki a kanta ba da na so na gwada mata koni wacece.
Wani irin kallon mamaki kawai yake masu take idanuwan shi suka rikide zuwa ja
kamar gauta a lokaci daya.
Yace cikin wani irin murya please get out in my house before i take a desition
on you.
No no UF kada kace zakai min haka please already mun riga mun gama maganan nan da
kai ko.
Tazo har inda mukw a tsaye tana cewa tare da nuna ni da hannun ta wa an yar
kauyen matar taka bata dace dakai ba don tafi dace wa da masu gadin ka kawai.
Fauuuu muka ji kara mari tace ido rufe maza su kwashe subar mai gida mara sa
kunya fitsararu ko mata sun kare a duniya mai zaiyi da ita mace da taje london ta
gama watse wanta zai dauko ya kawo wa kanshi fitina a gida .
Tas yai masu suka fice simi simi da kunya wai su tantire sai gashi su hadu da
wanda ya fisu iya fitsara yai masu tas gaban matar shi.
Wanan karon tare da tsaraban ahi ya shigo gari don koda su salma zasu wuce wata
hilux data kwaso mai kaya daga airport tana sauke kayan a kofan gidan mu.
Ana shigo da kayan ciki yai tsaye yace Amira tafito ta wuce zuwa gida sai ya zo
zai nemai ta a gida.
Aiko Amira ta ce yaya may kake nufi korana zakayi don munafukar matar ka tai muna
hadi a gurin ka hau kazauna akai.
Babu inda zan tafi sai ka bude kayan nan a gabana kowa ya gani haka wancan karon
nazo nai zaman banza komai baka ba.u ba yadda ka saba ta kwashe takai kauye
inda,ba,a san darajan su ba ma.
Amira waiko anya kanki daya kuwa, ina dai gani kanki ba guda bane kawai don hakan
da kikeyi abin naki ya zarce sanina gaskiya.
To bazan bude ba kuma maza ki kwaso kayan ki tun ban bata maki rai ba a gidan
nan.
Idan Fatima ta kwashe abina nakine ta kwasa ko nawa ina ruwan ki da kayana Amira
Fatima matatace ko kina da abinda zakiyi kan zaman ta matata.
Yaya ta furta tana mashi kallin mamaki tace kan Bintu kake fada min haka yaya
Bintu fa Bintu dai.
Yace Idan na kara jin kin kira Fatima da Bintun nan da kuke kiranta dashi don
rainin wayo wallahi sai kinyi mamakina Amira fito kawai ki tafi gida zan zo zamu
hadu agidan ai.
Haka yai mata kora na kaskanci kan abinda tai min wanda tun yana can Bashar ya
fada mashi komai duk irin halin da muke ciki da Amira a gidan, da bayana ranshi yai
matukar baci shine ya zo muna a bazata batare da ya fadawa kowa zuwan shi ba.
Wanka ya shiga don ya rage gajiyan jikin shi ina kitchen ina hada mashi abinda
zaici na juya zuwa dakin na shi inda na samu ya fito daga wanka na yana saka kaya
a jikin shi.
Jin motsin shigowa yasa shi dan juyowa yana kallo na tare da sake murshi a fuskan
shi.
Yace batare da ya dago kan shi gare ni ba mai yasa kika boye min halin da kuke
ciki a gidan nan da Amira.
May yasa tun wancan zaman baki fada min ga irin rayuwan da kukayi da ita a gidan
nan ba.
May yasa ki ka bari Amira ta tara yan iska suna wullakanta min ke ne haka a cikin
gidana.
Ya dan dago kai kamar a fusace yake magana yace may yasa zaki boye min irin wana
mugun halin da Amira taita gwada maki.
Nace yaya Anty fa yar uwatace komai tai min kanta taima bawai, ni kadai tai wa ba
don wata rana zai bata mata rai yadda tai min din.
Nace yaya duk abinda Anty ke min a saboda kaine don taga ban cancanci na aure ka
ba saboda matsayina bailai na hakan ba.
Sau dayawa nakan rasa laifin may nai wa anty Amira take min haka yanzu , sai da
ta fada min akan gangancin da nayi na auren ka yasa take min wanan halin.
Hawaye ya gangaro min a fuskana nace yaya sadauki nasan nayi gangancin auren da
matsayina baikai gare shi ba.
Haka kuma wanan ba shine irin rayuwan da ya dace dani bayar tallakawa kamata bata
dace da irin ku diyan masu kudi da matsayi ba a duniya.
Ya sadauki kaima kanka kasani bankai matsayin da za,ace ka aure ni ba kasani ba
irina ce ta dace dakai ba a gidan nan kamar yadda anty Amira ke fada min nima yanzu
nasan gaskiya take fadi don ban kai matsayin hakan ba a gare ku.
Yaya kayi yadda yan uwanka da masoyan ka ke son ganin ka tare da,diyan attajirai
irin ku masu matsayi a duniya bani yar takawan kauye ba Fatima.
Ba so tsakanina da kai sai zumunci na wa yanda suka tashi a daki daya irin na
yan uwantaka kawai.
Kamata yayi ace na auri maigadin gidan ku ko wani dan aikin gidan ku wanda baida
matsayi irina.
Sai faman kallona yakeyi kamar talabijin da mamaki ya lura ina a cikin damuwa da
kuncin rayuwa mai yawa don bai taba ganina acikin irin wanan yanayin ba haka.
Sai na fashe da wani irin kuka mai tsuma zuciya a lokaci guda na durkushe a bakin
gadon shi ina rusa kuka.
Cikin kuka nace Allah kadai da mama suka san dalilin wanan hadin da sukai muna.
Amma da zaka daure ka auri wacce tafi dacewa da zama a matsayin matar ka hakan
zai matukar saka anty Amira farinciki a rayuwan ta.
Hankalin shi yai matular tashi a lokaci guda yace tabbas Allah ba zai yafe min
ba Fatima tunda nine yakamata na daukakaki a idanuwan mutanen duniya tun farko
Fatima amma na kasa yin hakan.
Matsalar duk nawane da na kasa fitowa fili na nuna cewa ina matukar son matata
batare da duniya na mata kallon wacce aka tilsata min da ita ba.
Dole ne komai yacanza daga gareni yadda kowa zai iya fahintar Fatima ta wuce
yadda suke tsanmani a gurina.
Ahankali ya tako zuwa inda nake a tsugun ne ina kuka shima ji yake kamar ya fashe
da kuka a lokacin.
Ya dago ni tare da kokarin mikar dani tsaye ya rigumay ni zuwa jikin shi muka
zauna saman baki gadon shi a hakan.
Yace Fatima ki kwantar da hankalin ki ki saurare ni dagani har ke zan iya ce hada
mu akayi amma kuma ba bisa kuskure ba.
Maji ta fahinci kiyayyan mu ba kiyayya bace illa kainace mai wani sabon launi ta
hango abinda mu bazamu ita hango aa kan mu bane a lokacin.
Fatima komai nawa ya canza a rayuwana adan zaman nan da mukayi dake tunane yanayi
da komai nawa yanzu ya canza min a dan lokaci guda.
Don haka ki fitar da zance su Amirah da wanan salman a ranki ,kimai da
al,amarinki ga ubangiji don shi yafi mu sanin me ke boye yafi kowa sanin abinda
bamu sani ba gaba dayan mu.
Sannan ina son ki saka a ranki daga yau ni Umar faruq sanda ina sonki Fatima,
ina kuma kaunar ki fiye da tsanmanin ki Fatima ke alheri ce babba a gare don ko
nina tabbatar da hakan da kaina.
Ina maki so na hakkika Fatima wanda ban taba tsanmani akwai wata mace bayan uwata
da zanyi wa wanan irin son ba a duniyan nan.
Ni Umar Faruq nai alkawari har ga Allah zan rike amnan da mahaifana danaki suka
bani akanki zan .
Zan taimakawa rayuwan ki naga kinyi abinda kikayi niyaryi, zan taimaka maki tako
wace hanya inga burin ki yacika akomai.
Ki sani yaya sadaukin ki nai maki alkawari Fatima muddin muna a raye insha
Allahu zan maki komai don wanan Umar din zuciyar shi da gangan jikin shi wanan
kirjin da kike son kwanci akan sa duk nakine ke kadai Fatima zarah,.
A kullun zaki kwanta akansa kuma zan share maki hawayen ki harta inda baki zata
ba Fatima.
Fatima muddin ina a raye duk abin kike so shi zan maki don haka ki share
hawayenki Umar nakine ba wani wanda zai shiga rayuwanki ni da ke , sannu a hankali
muddin ni mijin kine kina a matsayin matata zakiga gurinki suna cika daya bayan
daya.
Yana dan buga min baya yake fadin Sadauki nakine zan maki duk maganin matsalolin
ki don zan share maki hawayen ki.
A hankali na dago kaina na kara shigewa cikin jikin shi ina fadin cikin kuka
nagode yaya sadauki Allah yabar min kai a rayuwana yabamu hakkurin zama da junan
mu.
Yace Amin Fatima nima nagode Fatima da kika fahince ni a cikin sauki tashi muje
ki bani abinci naci yunwa nake ji banci komai ba tun jiya dasafe don kawai nazo
naci girki yar matata naji dadi.
Murmushi nayi tare da mikewa ina gaba yana bina a baya mukaje falon sai da ya
zauna na zuba mai abincin ya fara ci.
Mikewa nayi na fara gyaran falon da suka bata kaca kaca wanda a kullun sai nayi
gyaran shi fiye da sau uku suna batawa.
Yana cin abinci yana kallona a fakaice yana tinanen ashe zancen da bashar ke fada
mai Fatman shi ta koma kamar boya a gidan kan abinda Amira ke fada mai.
Bayan na saka kamshi ko ina yafito neat ya mike ya dawo saman kujera yana waya.
Daki na shiga na kara wanka na gyara jikina tas nafito falon ina kamshi inda yake
zaune na nufa da hannu yai min nuni da nazo saman kujeran da yake a kai na zauna.
A hankali yakai hannun shi saman jikina yana waya yana wasa da part din jikina a
hankali.
Yana gama wayan yake cewa idan kin huta zuwa dare ki bude kayan nan da nazo da
su, naki ne sunfi yawa daga ciki sauran zaki iya zabawa maryam da Amira sai kuma
wanda kika so aba.
Nace mai mama fa yace atamfar Holland ce sunan nan zaki gan su kema ki zaba tunda
naga kina son su sosai amma ki min dinki da zai fitar min da suran ki a fili.
Nace kai haba yaya abinda ake fadakar da mutane ba,a son anayin su yanzu yace ba
ani zaki sawa ba ko wani ne zakiyiwa kwalliya bani ba.
Nace an gama yaya indon wannan ne kawai mikewa nayi na shiga fitar da kayan ina
matukar yaba yadda ya iya zaben kaya haka kamar mace.
Gaba daya gidan su sai dana fitar wa kowa da nashi kaso har yaran mummy da suke
kanana sai da suka samu tsaraba haka yasani fahintar tafiyan da yayi akwai sa,a
sosai a cikin shi ke nan don haka yakeyi duk yai tafiyan da yayo nasara zamu sha
tsaraba masu tsada muma a gidan.
Ranan kan naji jiki a gurin yaya sai dai daurewan danayi kawai don iyan zu na
fara sabawa da halin shi ko.
Da safe bayan mun karya ne yafita zuwa kai tsaraba gida bayan na rubutawa kowa
suna a nashi yadda zai gane.
Ranan kowa ya fahinci na fara jan ragamar aure na a gidan sadauki don ganin kayan
kowa da sunan shi a jiki.
Dakin su Umma cewa mama Asiya tayi waiko kin gane cewa wanan yarinyar itace ta
zabawa kowa kayan nan don ga suna kowa a jikin su .
Rukaiyya ta tare su da cewa amma kuma mama ai atamfan duk suna da matukar kyau
wallahi don ni sun bani shawa,awa sosai wallahi.
Ke rufa wa mutane baki ke may kika sani ba sai tazabi na iyayyen ta yafi kyau ba
ta bamu matasa kyau.
Kai haba mama wallahi haka baida kyau fa ina laifin Fatima gida su yaya ko tsuki
sun taba kawo maku ne yakamata ku daina irin wanan halin wallahi inji yaya Sagir.
To sannu uban mu inji Umma yan uwan naka zakaiwa gori kuma don bakin kwadayi.
Mashayi dai ne ba wata tsiya ba can don har yanzu ba fasawa yayi ba ai tana cikin
fadin haka sukaji hayaniya daga tsakar gida.
Nafisa ce tayo mugun sha take ta watsar da duk abinda tagani a waje da sauri suka
fito hardasu mama dake dakin su cikin tashin hankali.
Ga kayan jikin ta yai futu futu sai ashar take zubawa tana fafin nagane duk
munafukaine gidan nan don babu wanda ke sona.
Sai kuma tasa wani ihu kamar wata yar daji da taje farauta tace yau zan ci kazar
uban duk wanda ke gidan nan munafukan banza xa wofi kawai.
Kuke nan kullun ku shige daki kuna kulla yadda zaku kashe UF ko wooo UF ko yafi
karfin ku wallahi sai UF up up UF buga muje yayana ikon Allah .
Umma tafito rai a bace ta nufe ta tana fafin Nafisa abin naki kuma ya koma
haukane ko may .
Tace Umma ni kika ceqa ma haukaciya yau ko zan gwada mamu ni ma ma mahaukaciyace a
gidan nan saiko ta dauko tabaryan dake yashe a tsakar gida tayo kan Umma gadan
gadan dashi.
Ganin da gaske zata rotsawa umma ne yasa umma juyawa da gudu saiko ta fadi kasa
ku caaa gap da ta rotsa mata Sagir dake daki yafito jin yadda kowa ke ihu yayo
kanta yakai mata shuri sai da ta fadi kasa takife bakinta ya fashe.
Kara dagowa tayi tana fafin wallahi yau sai na kashe ka gidan nan ni zaka daka
haka ?
Nan ya samay ta yai ta jibga saida aka tare shi ganin haka yaran mummy suka sa
ihu maji ta jasu zuwa dakin ta taboye su a ciki.
Yaran duk sun tsorace Umma tayi tayi ta tashi abu yaki kafa ya rike mata ashe
tayi targade ne ba,a sani ba.
Ganin haka yaran ta suka saka ihu suna kuka neman taimako ga uwar su.
Mama Asiya ta bugawa Maigidansu waya yazo gida ba lafiya suna tare da sadauki
dayaje gurin shi kasuwa.
Tare suka iso gidan cikin rudewa gashi an taru akan umma sai hawaye take tanaji
kamar zata mutu.
Mummy ma dawowan ta ke nan ta samu wanan tashin hankalin daukan mama akayi dakyat
zuwa asibiti sadauki da sagir da mama.
Yaran mummy suka fito dakin a tsorace suna ganin uwar su sukayo kanta suna kuka.
Ta rugumay su tana fafin yau kuma wanan iftila,in ne yazo muna agida haka kai
Allah ya kyauta kawai.
Nafisa na cikin dakin uwarta sai ashar take ta zubawa da tonon asiri wa uwar ta.
Alhaji yana tsayevsai zufabke karyo mashi na tashin hankali mama da mummy suka
nufe shi suna cewa yashiga ciki ya zauna kada kuma yajawa kan shi matsala.
Sai wani lokaci aka dawo da Umma duk ta jirkita ga uban bandejin da aka lailaiye
mata kafa dashi.
Baba najin muryan su sun dawo yafito da sauri yace Atika kada ki shiga min gida
dauki mahaukaciyar yar ki kubar min gidana.
Cikin yashin hankali aka shiga bashi hakkuri amma ina ya hau baji alokacin da
kyat sadauki dasu mama suka samu ya koma dakin shi.
Umma tace tana kuka ai dama nasan shetine wallahi sai Allah ya isar muna duk wanda
keda hannu cikin lalata min rayuwan yata.
Kai kaji kuma wani wauta wa zai tsa yiwa Nafisa wani sihiri kuma ga abin kwarai
ba ai masu ba sai wanan barkatatan taki.
Haba hjy kubura a dai bar zancen ai Allah ba azzalumin kowa bane duk mai wa wani
sheri ai zai girbi abinshi tun anan duniya don Allah bai barin