Author : Zainab Idris Makawa Seenabu Category : Complete Novels
wayan Raiha ba ya saka layin shi
yakira nan ya samu nomban ta.
Sun dawo arewa kwanan su daya a garin sokoto takaita garin kakan nin ta ta kwana
washegari ta dawo sokoto ita dashi dake jiran ta a birnin kebbi.
Maman ta taga ta sake maimakon taje kauye tayi baki amma sai wani haske ta dan
kara sai dai tayi dan rama amma fa tayi mata kyau a fuska sosai.
Yanzu ke Raiha kada dai kinje kin cinye ma yan tsofi kajin su wanan irin haske da
kikayi haka anya kuwa ba barna kikayowa tsofin nan ba.
Raiha kuwa sai rankon barcin wahala takeyi don sai yanzu ta samu hutun wahalan
da tasha gurin Nasir a can Iko.
Sai dai shi bai sani ba ta riga da ta yanke a ranta cewa ta gama zama dashi ke
nan don yai mata wullakanci a can dama lalaba shi tayi har ta samu su dawo arewa.
****** ********** *****
Ganin yanzun ba wani ciniki take samu ba sosai yasa ta yanke shawaran samun dan
almajirin da zai dinga mata talla tana bashi abinci da dan kudin sabulu kamar yadda
da yawan almajirai sukeyi yanzu.
Duk almajirin da ya shigo zatai mashi tayin talla amma sai su zille suce malam
ya hanasu yin talla ko kuma suce dama shara ne ko wanke wanke zasu yi amma ba talla
ba.
Sai wani yaro ne tasamu yace mata zai yi Allah ya taimaketa yaron yana da kan
talla sosai don da yafita kamar ya kifar ne zai dawo ya kara wani.
Haka yasa tagane fita da sana,a waje yama fi cikin gida sosai samun ciniki .
Maigidan ta yaga almajirin yai mata magana akan ta dai kula da bashi hakkin shi
don kada Allah ya tambaye ta akai.
Amma,saboda dadin baki irin nata bata bari yakai karshen nasihan shi ba ta shiga
bakinta akan zancen.
Maigidan dai ido ya,sa mata baice mata komai ba sai cewa yayi bani abinci nashi
kada na makara zuwa daukan karatu.
Yana cin abincine yaran shi suka zagaye shi suna fada mashi makarantar su ance
a,sai masu shocks da takalma.
Yakai loma,a bakin shi yana cewa aiko sun dauko min aiki yanzu hada kudin safa
da takalma ai aiki a cikin wanan daman da ya fara.
Kuyi hakkuri insha Allahu zan sayo maku nan bada jimawa ba da yardan Allah.
Yana gamawa bai tsaya jiran komai ba yafita zuwa gidan babban malamin shi inda
yai karatun allon shi.
A nan yake zuwa daukan karatu gurin malamin duk dare idan ya,dawo daga gurin
neman kudin shi.
Yana fita ymta jawo bankin kudin ta tafara lissafawa inda taga irin ribar da ta
samu gurin tallan almajirin ta.
Tayi murna kwarai don ba karamin cabawa tasamu ba ga wanan tsarin sai fadi take
ai wallahi mama ta taimakeni da wanan shawaran nata.
Don gashi kwana kadan na hada,waban uban kudin haka nan ta,ware nata ta cire
ma,almajiran ta nashi.
Har yaran sukai barci amma ita hankalin ta yana ga sakan zucin da takeyi itta
kadai a lokaci, na ganin ta hada kudi ta sai fili da sunan nata.
Sai karfe goma mijin ta ya dawo gida ya samu yaran saman shimfidan da ya tashi
ga sauro na cizon su.
Yacee haba maryama da wannan sauron kikabar yaran nan haka a cikin shi suns cizon
su gani ba kudi gareni ba idan maleria ya kama su da,wani zanji.
Sayen abinci ko sayen magani da zuwa asibiti gashi yanzu zazzabi idan ya kama
mutum kamar ba zai barka,ba sai ka hada da,asibiti dole ko chemest.
Nan ya shiga kwasan yaran zuwa cikin dakin kwanan su gaba dayan su saida ya kwashe
su ya kaisu daga ciki.
Maria na gama abinda take ta nemi guri ta kwanta don dama a ganiye take don tun
safe bata huta ba tana gudun tai barci masu sayen ruwa ko wani kayan sanyi su
shigo.
A gaakiya ta godew haduwan ta da Muda almajirin ta don yaro ne ma hazaka gashi
da amana.
Koda gurin lissafi tai kure zai dawo mata da canjin ta, ya bata abinta, bai sa
ta gode mai ba.
Ko da daga gurin talla ya dawo bata barin ya dauki abinci komai yunwar da yake
ji.
Sai yai mata shara da wanke wanke, da yan sauran aiyukan gida kafin ta sallamay
shi.
Hakan ne ke batawa yaron Muda rai yana yawan yiwa yan uwan shi almajirai korafi
sosai.
Wanan shine matsalar da ke damun yaron mai mata talla koda zai makara ga karatun
shine sai yai mata aiki bayan kuma akan talla sukai alkawari kawai dashi.
Wata rana yana fita daga tallan ne sai gashi ya dawo jiki na makyarkyata yana
jin sanyi ba lafiya.
Maimakon Maria ta ji tausayin yaron sai cewa tayi shine baka sayar ba kadowa
min dashi ya tsiyaye ga banza.
Cikin rawan sanyi yaron ke fadin banda lafiya ne maman Abba sanyi nake ji sosai.
A je katafi tunda yau baka son yin tallan ke nan nagani, maman abba in kina da
magani don Allah ki bani nasha.
Tace cikin tsawa banda shi kaje gurin malamin ku yabaka shida ya dauko ka mana.
Yai shiru kamar mai nazari can yace don Allah ki taimakeni da koda cikin kudina
ne na biya shago nasai magani.
Babu su tafadi a cikin fada da,dan tsawa yaron yafita yana dan makyarkyatan
sanyi don fever ya damay shi.
Yana zuwa makaranta ya rabke da ciwo maleria ta kama shi sosai nan malamin su ke
tambayan shi ina kudin tallan shi ya bayar a,sayo mai magani yasha.
Da kyat yaron ke iya magana yake cewa na tambayi matar tace wai babu kudin.
Malamin ya hasala yafito yana tambayan wayasan gidan da Madu ke talla ya aike
shi.
Suka yaran wasu sukace sun sani nan sukatafi gidan don su karbo kudin shi hannun
maria.
Amma sai tace a tafi ita babu kudi a hannun ta sai dai idan ta samu zata aiko
mashi dasu.
Almajiran basu fita ba suka tsaya yi mata tsageranci, akan sai ta bayar da, kudin
sukai wa malamin su.
Sun dade basu samu ba dole suka bar gida taki bayarwa kuma tabi su da zagi.
Suna fadawa malamin yace kada wanda ya koma gidan subarta da Allah a bar
maganan.
Shi yakai yaron asibiti akai treating din shi ya biya kudi har yaron ya samu
sauki.
Bayan Muda yaji sauki yaki zuwa gidan ta nan almajirai yan uwan shi kewa
makwaciyar ta hiran shi tace akawo shi ta dauke shi aiki.
Ita ta rike yaron zaman amana kamar itace ta haife shi haka yasa Maria jin wani
irin kishi kamar zatayi hauka
****** ******** ******
Kamar yadda mai masa taiwa Maji alkawari haka din ne don batai sanyi a,gwiwa ba
ta shirya sai wani kauye can gaba da kauyen su gurin wani malami.
Malami irin malamai na kwarai bai damu da wani kudi ba don a kauye yake kuma ita
dashi yan uwane ta mahaifiyar su.
Yana ganin ta ya shiga murna da nuna jin dadin ganin ta nan yasa ai mata girki
na musan man kamar yadda yan kauye suke yi idan sun ga bakon birni yazo gurin su.
Sai da dare suka samu kebewa dashi da ita suka kara gaisawa sosai, nan take,
sheda mashi dalilin zuwan ta gurin shi.
Ya jijiga kan shi yana cewa matsalar ku ke nan yanzu yaran birni don kwanaki
akwai wani da yazo tun daga kano har nan gurina akan wanan matsalar.
Amma yanzu ba abinda zamuyi sai dole munyi istihara don naga daga inda matsalar
take, don kinga ba dama muzo muna aiki inda muka dosa daban abinda ke damun shi
daban.
Don haka ki bari sai zuwa gobe da safe sai nai maki bayani, mai masa tai mashi
godiya sosai nan suka dan taba hira na yaushe rabo da junan su.
Washegari tun da,sauran duhu aka kaiwa gwago ruwa masu zafi tai wanka tana
fitowa ga koko mai zafi da kosai da masa irin tasu ta kauye da badin shi.
Tace wani abu sai kauye mu a,birni ai yanzune ma,wata mace ke gyara kwanciyar
ta.
Sai da ta karya tashiga ko wani lungu na gidan suka gaisa da mutanen gidan sai ta
dawo dakin da akai mata masauki .
Ba a jima ba malam ya,shigo gidan ya shigo dakin da mai masa take ciki suka
gaisa yai mata ban gajiyan tafiya da bakun ta.
Can yace Asmau nayi duba akan matsalar ku amma gaskiya akwai yar matsala a cikin
harkan.
Don shi wannan yaron gaskiya akwai hannu ga harkan shi.
Don tun yana karami aka soke shi don haka su abubuwan bayin kan sa bane.
Yaron nagani yana da taurari masu haske sosai a rayuwan shi don hakane akayi
kokari dakushe masa su don kada ya haska.
Anje anyi tambaya a kan shi amfadawa wa masu shi cewa zai zama wani abu ga
rayuwan shi shine suka,sa ai mashi wanan aika aikan.
Kuma al,amarin ga yadda nagani ba wai mutum guda bane yai masa haka ,a,a suna da
yawa kowa kuma da irin aikin da akai mai.
Ga miyar kifi aka bashi wanan abin shaye shayen yaci shi.
Matane da namiji guda sai dai ba zaso na fada maku su ba don gudun hadin hasu
mi.
Yanzun mu matsalar mu shine mu san mafita akan zancen mu san yadda zamu nemo
makaru mu kara wanan asirin na jikin shi.
Don muddin yana tare dashi ba,zai taba zama wani abin kwarai ba ga rayuwan shi.
Kin ga yadda nagani matar tana da yara uku a,raye shine dana farko a gurinta.
Su ma sauran diya matan nata biyu wallahi ba,a barsu ba don suma suna da nasu
asirin sai dai suyi ta zaman gida ba aure.
Koda ma an dace sunyi auren bazasu zauna ba zasu fito don zasuji auren ba dadi.
Yan da zaai sha rubutu ne kinga sai na rubuta maki wani rubutu ki fara,zuwa masu
dashi har uwar tasu tasha.
Kafin kwana biyu nan da sati biyu ki dawo lokacin na,shirya,sauran abinda da zan
baku.
Gwago tace zai sha mana malam ai kasan wanan dolene asan yadda za,a bashi yasha.
Yace kin san yanzu yayin izalar nan ta sa matasa basu son shan irin abubuwan nan.
Kuma mutane ne basu gane ba ai shi a addini musulunci da kike gani kur,ani
maigirma yazo muna da,warakan komai a cikin sa.
Malam zai sha yace to amma fa uwar ce zata sha tabasu da hannun ta,suma su sha
hakan zai dan kawo muna saukin abin insha Allahu.
Zanbaki abu biyu zuwa uku kikai masu sufara yi insha Allahu idan sunyi badai samu
ba in ma wani yakara kokarin yi masu sai dai ya koma ga maishi wallahi da izinin
Allah bana mutum ba su dai kada suyi wa wani sheri a rayuwan su.
Nan ya mike yaje ya hadowa gwago mai masa abubuwan fa,zai bata yace takaiwa Maji
da diyan ta Allah ya sauwaka.
Gwago bata tsaya ba ta juyo zuwa,sokoto a ranan sai dai cikin dare ta iso garin.
Don haka ta wuce zuwa gidan ta da abubuwan sai washegari take da niyar takawo wa
Maji su.
******* ******** ******
Washegari ba a zuwa makaranta don haka yaran kowa yana zaune falo tare da iyalin
shi.
Bintu tana daga ciki tana shiryawa don yanzu tagama gyaran guri don ita bata
gajiya da aiki ko kadan,
Idan kaga yadda part din maji yanzu yake kalkalkal zakace ba mutane a cikin sa da
yawa.
Wani lokaci har hajuya Kubura takanyiwa Maji ba,a tace hajjiya maijidda ki bani
wanan yar taki mana.
Wallahi ni dai yarinyar taimin bata,da kiuya ko kada,akwaita da tsabta ga ta,da
kwai wallahi.
Maji kanyi dariya,tace a,a kibar mi "ya ta,Allah ne yakawo min hutu ta hanyan ta
.
Bintu tafito falon duk suka bita da ido har maji din, sai maji ke cewa kun gani
tai aiki kuma harta gyara jikinta kuko kuna nan kuna bakin shiriritan ku da kuka
saba ace gari ya,waye mace bazatai wanka ba ba kuma komai kukeyi ba. Mutane suyi ta
shigowa suna,samun ku a haka.
Kai maji ko munyi kwalliya wa za muyi wa mutum ko saurayin kwarai baida.
Au sai da,saurayi ake kwalliya mace fa da kwalliya aka san ta ko yaushe don
abinda kuke yi anan shi zaku je gidan mazajen ku kuna yi.
Bintu ta dan zauna daga kasa sai cewa maryam tayi kai Bintu ke kullun kamar
bakuwa har yanzun baki saba ba ke.
Kila dai tsoro take ji a,a bata da tsoro wallahi, don ranan fa itace tafara zuwa
gurin yaya sadauki ta kama shi.
Aini wallahi ranan Bintu ta bani mamaki sosai wallahi, don gaba daya na tsike ni
a lokacin.
Maji wacce zuciyar ta ya sosu da zance amma sai take cewa ai Bintu tai kokari
wallahi sosai.
Toke halan waya fada maki anabawa mutum manja da gishiri ya sha idan yana haka.
Tace nima labari naji wata yar ajin mu tanayi cewa wai duk yadda mutum yasha maye
idan aga yai mashi yawa abashi manja da gishiri sai ya amaye su su rage mai aiki a
jikin shi.
Ikon Allah inji maji tace Fatima shine kika gwada ke kuma gashi kuma na lura abin
yai mashi amfani sosai don yasa yadan dawo cikin hayacin shi.
Amira tace wallahi aini duk mamakin Bintu ya kamani a lokacin don ni ba karamin
tsorata nayi ba don na dauka ma mutuwa zaiyi ai.
Kai sadauki Allah dai ka,shirya kayan ka amma sadauki bai min da ba,wallahi.
Yaro kai kadai Allah yabani namiji amma kuma kai ke sani kuka.
Maji ki daina mashi kuka don Allah adaiyi ta addua inji Amira ta fadi cikin
muryan tausayi.
Ai inayi Amira Alla dai ya,sauwaka kawai don na lura fa abin nashi yai girma
sosai ko ba yanzu yafara sha ba.
Shin tsaya dai in tambaye ki Bintu wai dai ko ranan nan ma da kikace wai kin fada
kwatane shine yai maki amai ga jikin ki wai.
Da sauri Bintu ta dago kai sai kuma ta dukar da kanta kasa don bata iya karya ba.
Da sauri maji ta dago kai tana kallon Bintu tace wai Fatima hakane ko kuwa?
Tace hakane Maji nan ta fada masu duk yadda abin yafaru da yadda ta samay shi a
kwance har shigowan ta gidan.
Shiru sukayi dakin suna nazarin zancen Bintu kowansu yana yaba kaifin
hankalinta.
Maryam tace shine da kika shigo baki fadi ba Bintu?
Haba Anty Maryam bayan nasan mama bata da lafiya shine zan fadi na kara mata
ciwon kai.
Bazan fadi ba gaskiya don ban son hankalin mama ya tashi, don ba karamin tashin
hankali zata shiga ba.
Baki gafa yadda yake bane nima da kyat na uya kai shi dakin shi kamar numfashina
zai dauke nake ji a lokacin.
Ikon Allah wanan yarinyar akwai ki da mugun karfin hali wallahi danice ai ihu
zan dinga kantarawa sai kowa yafito a gidan nan.
Da,sauri Bintu tace kai anty ai wanan rufin asiri ne ba abinda za,a bari wani
yaji bane.
Kinji ke mai cewa zakiyi ihu maji ke fadawa maryam hakana tace ai Bintu yarinya
ce mai hankali wallahi.
Ai kan inji Amira don akwai ta da dan banzan wayyo kun gan ta nan.
Sallaman mai masa ne ya dakatar su suka,shiga gayar da,ita suna mata ina kwana.
Maji tace a hajiyan masa ashe tafiyan naki ba mai dadewa bane har kin dawo ?
Nadawo hajiya dama tafiyan nawa ai donki nayi shi ba tafiyan kaina bane nayi.
Maji tagyara zama tana fadin ikon Allah ashe mu akaiwa tafiyan ke nan.
ZAINAB IDRIS MAKAWA
SEEENABU
IDAN BAKI BIYA BA KADA KI KARANTA HAKKIN WASU, PLEASE,,,,
Bayan gausuwa a tsakanin su sai kuma dan shiru yafara biyowa baya hakan yasa Maji
cewa yaran ku bamu guri mana ko.
A,a su zauna ai gara suji abinda zan fada da kunnuwan su don su fahinci maganan
da zan fadi da kyau.
Tsit yaran har
Maji su ka yi a falon bawanda ya koda dan motsa sai gwago ce tafara magana kamar
haka.
Na tafi kauye ne gurin wani malami amma dan uwana ne can gaba da kauyen mu.
Na samay shi akan zancen wanan yaron sadauki ne amma kuma sai wani magana ta
daban tafito muna.
Kin san yanzu mutane ba imani da tsoran Allah a tare dasu.
Kin san yanzun muna a lokaci, ga imani a baki amma ba shi ko kadan a zuciyan
bayin Allah.
Wai kuma a haka kowa ke son shiga aljannane , ga son duniya ya rufewa mutane
ido da zukatan su.
Wanan duniyan da ba bakin komai take ba ga mai imani da tsoron Allah.
Wai may kuma ya farune hajiyar masa inji Amira da take jin digon bayanin da
hajiyan masa keyi yai mata yawa.
Waiko kina da hankali Amira baki da kunya fa ke ko kadan ,ina ruwan ki da zancen
mu ne wai.
Hajiyan masa tace barta ai