Author : Zainab Idris Makawa Seenabu Category : Complete Novels
kwanta bai dade da kwanciya ba sai ga baba mama da mummy sun
iso suma.
A falo suka fara zama nazo na gausa dasu suke tambayana nake fada masu abinda
yakeyi ai sai aje asibiti baza a barshi a gida ba hakana bamu san may ke damun shi
ba .
Naji tsoro sosai a raina kada aje asibiti ace poison aka bashi fa yaci nawa ya
samay ni garin neman kiba na samo rama kuma.
Mun shiga inda yake kwance sai faman murdan ciki yakeyi sosai yana juyi mummy ta
dan dubashi tare da bashi tace Alhaji aje asibiti kawai.
Ina gefe daya a rakube hankalina a tashe yace No abari kila zai bari ai baba bai
yarda ba suka sashi a gaba ya tashi aje asibiti dai.
Inda nake tsaye idanuwana suna fitar da hawaye ya dan kalla yace cikin karfin
hali Fatima dauko min kaya na saka.
Jin haka suka fito daga dakin suka barmu a tare sai kuka nakeyi cikin karfin hali
bayan ya gama sa wando ya jawoni jikin shi yana cewa.
Ki daina kuka mana Fatima bakya son ki rasani ne ko ?
Ban bashi amsa ba na saka mai rigan tie shirt tare da dan shafawa fuskan shi dan
mai sai ajiyan zuciya yakeyi sosai.
Bashar ne ya leko yake cewa yagama ne mu tafi nace mai eh a lokacin ina rugumay a
jikin shi muka fito daga dakin da kyat yake tafiya.
Har sun fita bashar ya dawo cikin gida kaman zai dauki abu yace min a hankali kin
bashi maganin ne nace mai eh yace ok dama ance zaiyi amai ya wahala sosai kada ki
damu komai basu ganewa ai.
Shiru shiru suna,asibitin dashi muna gida da Iyya hankalin mi a tashe sosai a
lokacin dashi.
Mama ce ta bugo waya tana fada min in kwantar da hankalina likitoci suna kan shi
suna bincike yanzu haka.
A raina nace ina naga kwantar da hankali asirina zai tonu haka kuma daga
taimako .
Sai guraren sha biyu da wani abu bashar ta dawo gidan yake fada min an bashi
gado asibitin sunce wai canji ruwa ne ko kuma yaci wani abu a can wanda suke gani
kamar bai dace da cikin shi ba.
Nan yake ce min mama tace yazo yaje dani yanzun don suna son zuwa gida suyi
sallah su tinda yadan ji sauki .
Mun isa mun samay shi kwance yana barci har ya fada sosai bashar yake tambaya
baiyi aman ba ko sukace yayi har sau biyu bayan tafiyan ka ai.
Ina tsaye kan ahi na kura mai ido ina kallon yadda ya koma a raina nake cewa
wabda duk yai maka wanan asiri Allah ya saka maka.
Muryan mummy ne take fadin bari muje gida mu dawo sai azo maku da abinci nace ai
da a barshi Iyya tana can tana hadawa ai.
Sun wuce aka barni da yaya bashar basu dade ba maryam suka iso da mahaifiyar
yaya bashar din nan muka zauna atare dasu.
Sai dai mama tana bugo waya akai akai tana tambayan ko ya tashi a lokacin ko yana
aman har yanzu ?
Nace bai kara yi ba yana dai barci ne tace Fatima kada ki yarda a cika dakinbda
suruti kinji ku barshi ya huta please nace to mama.
Nan kuwa muka fara ganin yan uwa da abikan arziki harda ma wanda bamu sani ba
suna shigowa gaidashi.
Mummy tagama shiryawa tace wa mama su fito su zo mama tace haba hajiya kubura
kamar ban gode ma Allah ba ke nan ai.
Gaki ga matar shi da yan uwa a kan shi may kuma zan koma yi adduan mu yake bukata
kuma ya samu ko?
Allah dai ya bashi lafiya sai kun dawo agaida su mummy taji dadin hakan sosai
suka tafi tare da,Abdul.
Yadda yan uwa suka nuna mai yasa na gane cewa sadauki dan gatane sosai don sai ga
yaya Imiran da matar shi tare da abincin sukazo muna.
Nan dai guri ya cika makil Nafisa da kawayen ta sun shigo su ma nan suke cewa
yanzu Naffy ke fada muna mukace bamuga zama ba ai uwar dakin mu na cikin tashin
hankali.
Kowa yai mamaki jin abinda suka fadi may ye hadina dasu kuma sai cewa Raiha tayi
muna zuwa muna cika cikin mu ana muna,taron arziki ai dole ne mu zo gurin ki.
Wani likitane ta ke duba shi ko na kira P M O ne yazo da kan shi ya duba muna
shine dai.
Kowa yasan zasu uya don sunyi kamari wuce pmo ma balle director gaba daya.
Yaya Ahmed suka shiigo da matar shi jamila a lokacin dressing din ta kawai ya isa
mutum ya gane ko ita wacece.
Sai yatsune yatsune takewa mutane tana kallon shi tace au ashe shine ban ma taba
ganin shi bani.
Sosai na mayar da hankalina gurin su Nafisa da kawayen ta muna hira maryam sai
haushina suke ji da Amirah.
Suko yadda na ke tare da,su yai masu dadi sosai a ran su don sai jana suke da
hira ina dan murmushi.
An cika duk yan gidan su ne gungun gungu a haraban gurin falkawa yayi da karfi
yake kiran Fatima Fatima da sauri yaya bashar ya shiga dakin Abdul ne yakirani.
Na mike da sauri gabana yana faduwa idanuwa aka sako min caa da kyat nake tafiya
a lokacin.
Jamila matar yaya Ahmed bata sanni ba sai ranan take fadi au matar tashi ke nan
ashe ?
Ina shiga ya falka Bashar yana tsaye a kan shi lokacin na karasa gurin shi ya
miko min hannun shi yana cewa zauna kija min hannu na da kafa please.
Mummy ma tashigo dakin don ganin ya falka a lokacin tana mashi sannu da jiki ya
amsa mata da kyat da sauri ya dago yana son mikewa yace amai yake ji sosai da sauri
na dauko roban da aka sayo don ya dinga yi a cikin shi.
Amai yayi sosai bakikirin dashi nan hankalin duk wanda ke gurin ya tashi sosai
sai kawai ya rufe idon shi ya zama colarbs jiki ya sake mai da sauri na karasa ina
kiran sunan shi bashar yace na fita dakin .
Don kuka yaci karfina a lokacin ganin na fito ina kuka yasa mutanen da sauri suka
karaso jikin maryam na fada ina kuka tace may yafaru nace baya numfashi maryam da
sauri mazan gidan su suka shiga gurin shi dakin
Ina nan naga bashar yafito da sauri ya nufi gurin likita duk wanda ke gurin
hankalin shi a tashe yake sosai naji dadin su Nafisa da kawayen ta don sun nuna
damuwan su sai akaina.
Likita yazo da sauri suka shiga dakin yana fadin suma yayi bayan ya duba shi ai
hankalin kowa a tashe can sai ga baba da su umma sun zo.
Ikon Allah sai Nafisa ke fadin to baidai mutu ba balle aji dadi ba,azo ba sai
yanzun da akaji ance baya da rai yana nan daram.
Taba wasu haushi musaman yan uwanta amma babu yadda suka iya da halinya dole aka
saka mata ido uwayen dai sunji kunya sosai.
Yana falkowa yake fadin Fatima jamin hannuna da kafa please, sai da yaba kowa
tausayi a dakin na koma dole dakin duk da ga iyayyen shi amma ina dan matsa mai
hannayen shi da kafa a hankali.
Har dare muna tare da mummy don cewa tayi anan zata kwana amma sai yaya bashar
yace duk mu tafi gida dashi da sagir da Abdul zasu kwana gurin shi.
Hakana na kwana a cikin zullumi tun da safe washegari ina asibitin gurin shi.
Ance mutum mai yawan bautar Allah yakan zama wani lokaci kamar waliyi ne saboda
yawan ibadan shi.
Hakane ya faru da mama don tai sallah nafila tadan zauna tana tasbihi kafin a
kira sallah asuba tayi sallah.
Nan tai mafalki ana ce mata kada ki damu taimakon shi Fatima tayi amma zai mike.
Ta falka firgigi da ita tana cewa subbahanallahi Fatima kuma haka yasa zuciyar ta
zargin akwai wani abu a kasa amma koma may ye zata binciki Fatima din taji.
Sun shigo gaida shi da safe ne ta kirani gefe muka gaisai da ita can ta dafani
tace ki kwantar da hankalinki insha Allahu zai samu lafiya kinji.
Can naji ta dafani sosai tace Fatima may kuka ba saudauki ya shane haka mai karfi
don nagani a mafalki na yau.
Ras, ras gabana ya fadi uku uku lokaci daya nadaugo kai na da sauri na kalleta
tace ba boyo tsakani na dake fada min nace cikin kuka mama yaya bai bar sha ba har
yanzu.
Shine yaya bashar ganin muna yawan samun matsala ya koma gurin mutumin nan shida
maryam suka anso wani wanda zai amaye abinda yasha gaba daya a jikin shi.
Ina fadin haka na dago kaina kalle ta murmushi naga tayi ta dafani tace Allah yai
maku albarka Fatima kun karasa aikin dani ce ya dace nayi shi tun farko.
Kuma duk halin da kuke ciki na sani maryam ba ban sani bane amma tunda kikayi
yadda nake so dake rufin asiri a tsakanin ku yasa na ja bakina nai shiru dashi.
Tace ban son jin zancen nan a bakin kowa daga Allah sai ku da kukayi don koshi
kada ki yarda ya fahince ki don zai dauka wanan wahalan da yakeyi kashe shi kuke
son yi ba taimakon shi ba .
Don haka ki rike wanan sirin a ranki ki boye sirin mijin ki danaki a kowa kinji
Allah yai maku albarka nagode Fatima abinda nai hasashe ke nan tun farko akan ki.
Tare da mama muka dawo dakin yana zaune ya ramay ya fada sosai kamar bashine
yadawo bulbul dashi ba.
Ya samu sauki don aman ya tsaya sunce har cikin dare sai da yayi aman sosai
bakikirin dashi.
Yanzu sai barcine ya ke damun shi da ya dan falka sai ya koma yaci gaba da barcin
shi.
A sibiti muka fara azumin wanan shekaran da wata ya kama na azumi amma ya samu
sauki sosai.
Azumi uku mukayi a asibitin aka sallamashi ya dawo gida nan naci gaba da jinyan
shi da kaina.
ZAINAB IDRIS MAKAWA
SEENABU
IDAN BAKI BIYA BA KADA KI KARANTA HAKKIN WASU PLEASE,,,,
IDAN KUMA KIN BIYA KIKA TURAWA WANDA BAI BIYA BA MUN BARKI GA ALLAH,,,
Mun kai wani lokaci mai tsawo tare da yan uwa ana ta yaushe rabo a tsakanina da su
wanda yawanci duk wasan su akaina ne su na min wasan kanin miji.
Ganin yai shiru nasan halin abina bai faye son surutu mai tsawo ba shi sai dai a
dan yi ai shiru yasa na fahinci taron hayaniyan ya dan ishe shi ke nan a lokacin.
Na dan mike zuwa gaban shi nace tare da dan rakwafowa gare shi yana zaune ya rike
goshin, shi da hannu daya yana dan murzawa a hankali idanuwan shi a lumshe gaba
daya.
Jin muryana kusa dashi ina magana ina cewa yaya may za,a zuba maka ne kaci ?
Bude idanuwan shi yayi ya sauke a fuskana da nake duke gap dashi na kara cewa may
zakaci ne yaya?
Ya dan sauke min murmushi yana fadin duk abinda kikaga ya,dace dani ki zubo min.
Gurin dinin na tafi na fara hada mai abincin gargajiya wanda mun dade bamu ci shi
ba sai yau da muka dawo gida.
Tare da zuba muna ferfesun kayan cikin rago dana danyen kifi manya masu tsoka
sosai.
A plate daya muka ci abincin da yake ba,a saman table bane kowa yana kasa nan
kowa ya fara diban abinda yake so muna ci muna hira tsakaninn mu.
Nice na fara mikewa tare da dan fuskan tar yaya nace zan dan shiga ciki na kewaya
wai irin kallo yai min wanda yasa dul wanda idon shi ya kai ga kkallon a lokacin
sai yaji wani iri.
Don da ido yai min magana na taimaka mashi shima na shige dashi a cikin dakin
shi.
Hannu na mika mashi ya kamo tare da mikewa tsaye muka shige daki dakin shi muka
fara shiga sai da ya shiga wanka na fito zuwa dakina wanda nai watanni ban a cikin
shi.
Wani kamshi ne mai tuna min da abubuwan da suka shude a baya da dama kamshin
dakin nawa ya,tuno min.
Maryam ce ta biyo bayana muka zube tare da su a dakin nan na shiga wanka na
shirya cikin wani riga dogon milk color mai guntun hannuwa.
Na mulke jikina da kayan kamshi masu kyau da tsada na gyara na fito inda kowa
yake bayan nayi sallah.
Mazan sun fita zuwa masallaci mu matane muka rage a cikin gida sai ga Nafisa da
kawayen ya sun shigo taron mu.
Da murmu muka tari juna da su kowa yana mamakin dalilin shakuwa na da su darrr
ake zaune dasu kamar ana ga masu cuta a jiki ko kuma masu wani aikin kissa.
Sun fahinci cewa kowa yana jin haushi zuwan su gidan a lokaci da yake basu da
kunya sai cewa Nafisa tayi ni dai ba gurin uban kowa na taho roko ko maula ba gidan
dan uwana ne nazo dole kuma nayi yadda kowa keyi.
Nam suka so kaurewa da maryam da ita dama ba shiri tsakanin su tun gida Allah ya
kawo yaya ya daka masu tsawa tare da masu fada suka daina.
Kamar yadda Nafisa tace yadda kowa yayi haka zatayi don gidan dan uwan ta ne
hakane kuwa tayi.
Don mikewa tayi ta kwaso abinci gudan mai yawa ita da kawayen ta komai na gurin
sai da ta debo masu shi duk an saka masu idanuwa na ce su zo muje dakin Iyya can
muka zauna tare da ni dasu da ma maryam din .
Karshe suka shiga bamu dariya tun maryam na daure fuska har ta shiga dan
murmusawa hiran da sukeyi mun dauki lokaci da sune sukace zasu tafi ina tsaraban su
don shi ne sukazo tun yau kada a wawashe a barsu.
Nace tsaraban ku ya na hanya sai zuwa ranan Thursday ku shigo na baku naku
Raina tace kai uwar dakin mu walleh kada ki sa muyo tahiyar banza mu taho bamu ga
yan, kudin man, mu kuma bamu ga tsaraba.
Nace shim banita nice ku taho ba walleh na,sayo maku tsaraba tun can da sunan ku
na sayo shi .
Wani ihun dadi suka yi suka tafa tare da shewa shiya sa muka son ki uwar dakin mu
don ke dauki duniya simple ba ruwan ki da wani jiji da kai ko kyamatar halin mu
gare ki.
Nace kai amma dai anty akwai ku da wani irin magana lalura ta Allah shi yaye maku
ita bayan ita minana gare ku na kyama tunda dai nagani da idona kuna sallah to
miyarage kuma watan azumi anan kuka daukan abin buda bakin ku to mi aka so.
Nan dai mukai sallama dasu na fito na raka su har bakin kofa na juyo muna dariya.
Yaya Sagir yace Fatima ina kika kwaso wanan gayyan tsiyan haka,wa yan nan
mu,amula dasu ba alheri bane fa .
Yaya bashar yace ai kuma kaji matsalan mutanen mu ke nan wallahi sai a dinga
gudun mutum shi ke kara jefa su ga halaka sosai wallahi .
Yanzu yadda kaga Fmta sake da Fatima haka duk yadda ta juya ta zata bi don bata
kyamace ta ba kaga zata iya mata nasiha har yai tasiri a kanta idan ma wani magani
ne yadda da shakuwa zai sa ta yarda tasha koma may nene.
Shiru Sagir yayi yana sauraren maganan bashar yace bai kamata ace kuna nuna mata
kyama haka ba kujawo abinku ga jiki da sannu kuna mata nasiha kuna bata taimako har
ta gane gaskiya idan tana da rabon dainawa.
Amma gaskiya nisan ta kai daga mai shaye shaye yana kara jefa su ne a cikin
halaka kawai.
Shi kan shi yaya Sagir maganan tayi tasiri sosai a ranshi sai yake ji daga
lokacin zai yi kokarin ganin ya jawo Nafisa a jikin shi ya taimaka mata.
****** ********* ******
Washe gari muka tafi gidan su mama muka gaida su suke cewa ai da mu bari suzo su
samay mu su tare mu .
Yaya yace haba kai ai mune masu neman albarka a gurin ku dole muzo inda kuke mu
nema.
Mummy tazo dakin mama ta samay ni nan muka zauna ana hiran tafiyan mu tare da
mukayi a saudiya.
Duk hiran mu Amira na gefe a zaune mugun halinta yana cinta a lokacin bata saka
bakin ta ba.
Mummy da ta fahinci haka tace aike Fatima sai ki godewa Allah don Allah shi ke
azurta bawan ya duk sanda yaso.
Yau ga shi kece a wanan kasashen duniya ga yaran gidan mu da suka tashi a cikin
daula wasu ko Abuja basu sani ba balle wanan irin kasashen da kika shi ga haka.
Maji tace ai ubangiji miskarraziratin ne shi ke yin da yaso da bayin shi a duk
inda yaso.
Yanzun baga shi ba hajiya da gidan wani akakai wanan auren ai wani abin sai dai
mu hanga a cikin gari ko a makwabta kawai.
Amma yanzu kinga hikimar manya da mijin da matar komai gida,yake dawowa gaba daya
shine ai ake cewa duk abinda babba ya hango yaro ko ya hau sama baya hango shi.
Yaya sadauki dake gurin Baba tun shigowan mu yana mashi bayani akan tafiyan mu
irin nasarorin da yayo a gurin wasu masananta da ya saka hannun jari acikin su a
waje.
Yace to ke tashi mu tafi hakana ko mun bar iyya gida ita kadai mama tace yanzu
yarinya na zaune tana hira zakace wai ku tashi ku tafi.
Mummy tace yanzun fa ya san dadin iyalin shi bai son zama inda muke kuma .
Yai murmushi yace wallahi mummy ba hakana bane kawai da Iyya Rabi da muka bari a
gida ne ga kuma mutane suna zuwa taron mu har yanzu.
Mummy ai da zaku bamu daki a gidan nan sai munfi jin dadin zama a kusa da ku
dariya sosai yaba mummy har saida tayi