Author : Zainab Idris Makawa Seenabu Category : Complete Novels
wani mugun harara yace sai na karya ki a gidan nan wallahi yar iska
mai balain sa idon tsiya kawai.
Sai kuma yai shiru tare da kyatafa kawai ya dafa bango kan shi ya dukar a kasa.
Nace yaya kayi hakkuri bani son mama ta fahince ka a hakane wata rana kaji may
likita ya fadi a kanta.
A guji bata mata rai don dazara akai mistake watara zuciyan ya buga a lokaci guda
za,a iya rasata gaba daya.
Yaya kana son sanadin ka ace mahaifiyan ka ta rasa ranta kan bacin ran ka ne ko
yaya ?
Maimakon yai cikin mu da masifan daya fara yadda nai tsanmani sai naga ya dukar
dakan shi a kasa.
Ikon Allah sai Allah yau gani mukayi yata sadauki yana kuka kuka kuma mai ban
tausayi.
Yace maryam bani sha a ko ina sai ina garin nan i don't know why nakejin irin
haka kawai a garin nan ?
Idan ina garin nan in basha ba bana jin dadi rayuwana sam wallahi sai na dinga
jin kaman zan kama da,wutane.
Amma kudai tayani addua kawai Allah ya kawo min agaji ga halin nan.
Bana son ace sanadina uwata ta samu matsala a rayuwan ta ko kadan bani jin dadin
hakan idan na tuna.
Kuka ne ya dan fi karfin shi maimakon mu bashi hakkuri sai nima nafara kukan
abinda yasa Maryann itama kuka ke nan lokaci guda.
No no ku bar kuka please zanyi kokari naga cewa na daina hakan insha Allahu.
Nace yaya idan ka fara jin haka don Allah ka dinga nafila kana kai kukan ka ga
Allah don ka samu sa,idan jin hakan da kake yi.
Ya dago ya kalle ni ina makure a bango kaman zaiyi magana sai kuma yai shiru, ya
dade a haka yace ku shiga gida kada wani yazo ya samay ku anan.
Har na juya nace abinci fa yaya yace No kibar shi kawai I am OK.
Kuka sosai maryam tayi bayan shigan mu gida da kyat na samu na lalashe ta har tai
shiru tana tausayawa halin da dan uwan ta yake ciki.
Bintu fada min yaya kike gane yaya yasha ne wai ?
Nai murmushi na ce da farko idan kinga ya shigo da glass a idon shi to yasha
sosai ke nan.
Idan kuma kin gashi ya shigo ya zauna yai shiru kaman akwai abi dake damun shi to
abin yadan fara sake shine hakanan bai son yawan magana sai kasala kawai yake ji.
Sai kuma da zaran kinga yana bukatan abinci a gagauce to abinda yasha ya fita kan
shi ke nan sai kiga yana jin yunwa sosai.
Zakiga yana shiru shiru sometimes to yana cikin dan maye ne zai dinga zama kaman
wani salihi can dashi.
Bintu baki ganin kaman asirin da akace su Umma sunyi mashi a cikin gidan nan yake
kuma kilama a dakin shine ko makamancin haka ?
Nace sanin gaibu sai lillahi anty amma hakan kuma fa magana ce sosai.
Tace in hakane yabar gidan nan ya koma gidan shi mana da zama zai fi mashi sauki
nake gani.
Anty yaya zaibar gida baiyi aure ba?
Ke kinga alaman aure a gaban shine yanzu Bintu ?
Nace ai irin su mata basu gaban su anty duk matar da zai aura matsayin baibar
wanan rayuwan ba sai tayi hakkuri wallahi.
Don bata gaban shi idan yasha kuma sai dai yai ta tabara yana zubar da kiman shi
a idon ta da jama,an da suke tare.
Wai ke ina kika san wanan halaiyar tasu ne haka Bintu ?
Murmushin takaici nayi nace a gurin mijin mahaifiyata mashayine shima amma shi
irin shan nan na yan kauye yakeyi mara fasali.
Nan nai ta bata labari na yadda mamana take hakkuri tana kuma nema mashi maganin
hakan ?
Nisawa tayi tace shiyasa lokacin da su Baba Sani suka hana yarsu daga baya banji
haushin su ba wallahi.
Don yau babu wanda zaiso ace nashi na cikin fitina ko tashin hankali haka ai ?
****** ********* ******
Washegari Mama ta tilsata mu kan sai mun tafi gurin buki don ayi kamun amare damu
tana fada take cewa, ban san may yasa baku son yin zumunci ba wallahi.
Zumunci da kuke gani ba abin wasa bane wallahi don igiyace mai kai mutum aljanna
idan Allah yaso.
Amma rashi sanin darajan shi yasa kuke sakaci da shi alhalin gaku Allah ya baku
yan uwa bila,adadin a gari babu gidan wanda kuke zuwa kullun kuna kulle a gida
kaman kayan wanki.
Ba don mun so ba muka fara shiri bayan sallah azuhar zuwa gurin sa lalain yan
uwan su da za,ayi a family house din su na diyan kannen baban su.
Ga ba dayan mu dogayen riguna muka saka muka daura dan kwalaiyan su akawunan mu.
Shigar tai matukar karban mu sai dai matsala motar da zata kaimu ce babu a
lokacin haka yasa yaya sadauki yace mu bari ya kaimu da Amirah tai mashi magana.
Amirah ce agaba tare dashi mu muna baya a zaune sai dai ban san yaya akayi na
zauna a setin mirror shi ba na gaba.
Maryam ke fadi wai yau kan sai mun sha surutu a gurin mutane yaushe rabon da
naje gidan nan ni.
Amirah tace ni wallahi ba,son zuwa ne banyi ba yadda ake damun mutum yaushe zaiyi
aure yake damuna.
Daga inda nake zaune nace kai mutane akwaisu da daukan wa rai shifa aure kamar
rayuwa yake idan ya tashi koba shiri sai anyi shi haka ma rabuwan shi idan yazo ko
bashiri sai anyi shi.
Dago kan da zanyi naci gaba da magana muka hada ido dashi ta glass din motan
yadda naga idanuwan shi sai naji gaba na ya fadi daga haka naja bakina nai shiru
ban kara magana ba don duk na dago kai dashi nake arba sai ma na daina daga kan
nawa kawai.
Tun a kwanan gidan muka fara ganin dandazon motacin mutane da sukazo gurin kamun.
Wata mata tazo da motar ta shige gaban mu maryam tace shegiya mu akewa kurin mota
mima watarana insha Allahu ki gan mu da namu.
Nace kai anty kin rage mata kaya bata masan kinayi ba ita, Allah Bintu inason
naganni da mota ina ja wallahi.
Nace in Allah ya nufi ki ja sai ki gan ki dashi kuwa ai tace wai da su Umma sun
mutu ranan.
Nace su kuma ai zaman su ke nan hassada wallahi basu ko tsoron haduwan su da
Allah.
Allah suka sani aida basuje gidan su Bashar suke auren maryam ba inji Amirah.
Da sauri ya juya gareta yace kamar yaya wai har muka isa inda zamu sauka tana
mashi bayani haka yasa bamu fito daga motan ba sai da tagama mai bayanin komai
yadda akayi.
Mutanen dake tsatsaye daga waje sun matsu sugs ko suwaye a wanan haddadiyar
motatar haka ga shi na cikin motan basu fito ba.
Sai da suka gama magana ya bude muna tare da tambayan mu karfe nawa zai dawo ya
dauke mu Amirah tace shidda daudai yaya.
Nice na fara sako farin kafa na a waje daga gefen da nake zauna sai wata tace dama
nasan wasu special ne daganin wanan uban motan haka sai gidan gwauna, muna fitowa
ashe su Rahaman shi ce a tsatsaye nan shima ya hango su,
Kiran mu yayi muka dawo gare shi daya bayan daya yake muna magana kowace tana
juyowa da dariya ganin ya gama magana da kannen shi yasa nima na juya zan wuce
nabisu sai yace Fatima nace naam yaya yace zo nan na karasa gaban shi.
Yace don Allah kada kiyi masu kayanci agurin nan kiga dai duk ido akanku yake.
Maganan shi ce tasani dariya a lokaci guda wanda mutanen dake gurin suna zaton ko
wani maganan soyayyane yake fada min hakanan.
Yana fadin haka yaja mota yana murmushi duk suka bishi da idanuwan su caaaa kowa
na son ace itace ta mallaki aana haddaden guy din mai kyaun dan maci ji.
Abokan Rahama da yan uwanta ke ce mata kai amma gaskiya kinyi hasaran miji ko
dai wanan yarinyance zai aura ne?
Tace a kufule kamar
yaya zai aureta anfada maku anfasa zancen namu dashi ne halan .
Nan suka shiga gaisawa da mutane yan uwa da abokan arziki ana ta masu sheri don
yau bukin gidan su ne yasa su fitowa.
Buki yayi buki duk guri ya kicimay da kida don an fito da amare su hudu ne gaba
dayan su a filin.
Muna tsaye gefe sai kallon amaren muke gwananin ban sha,awa nace anty Allah ya
nuna muna naku muzo musha bidiri muma.
Ameen ke dai Bintu inji maryam itako Amirah cewa tayi nifa duk wanan abubuwan
basu damay ni ba fa.
Nace nima nafison in zanyi aure aimin walima haddade wallahi duk yafi wana
gwatsale gwatselen da mata da yara keyi.
Ji mukayi wai ana kiran dagin amaryam su Amirah su fito suyi rawa a fili basu so
fita ba kuma banyi tsanmanin zasu jani tare dasu ba sai ji nayi maryam ta jawo
hannu mun shiga fili tare ban iya rawa ba don ban ma,taba yi ba don haka takawa
kawai nake yi a hankali.
Kaina a duke naga su maryam su falle jakkan suna min liki take guri ya hau ihu da
sowa sai tambaya mutane keyi wacece ita da suke mata likin kudi haka?
Komai namu a gurin a natse muke abin mu cikin nuna sanin ciwon kai da kuma
tarbiya.
Muna gefe mu kaji guri ya kaure da sowa maryam ke tambayan ko su waye wata tace
wai ance wasu mashaya ne yan uwan su amaryan yan mata suka zowa kawarsu kara.
Innalillahi wacece kuma maryam taja min hannu Anty Amirah na gaba muka leka
Nafisa ce da kawayen ta suke wani irin rawa gasu sunyi shega zakace akwatawan ghana
ne su guri ya rude da sowa masu tir da Allah waddai suka shiga bakin su.
Daganin su a buge suke don rawan ba rawan kai sake bane har gaban samarin da suka
shigo suke shigewa.
Kiran wayan da sadauki yaiwa Amirah yasa mu saurin barin gurin muka fice a filin
gada ma agan su ace yar uwar su ce.
Mun shiga mota su Amira sai yankan fada sukeyi suna tir da Allah waddai da halin
rayuwan Nafisa.
Maryam tace yau maganan nan sai yakai kunnen Baba ai akwai magana agidan nan yau
wallahi.
Umma tagama jin kunya da nauyi ya agaban su fa su Nafisa ke wanan rawan tsiya
waisu ga yan iska.
Allah dai ya shirya su damu baki daya nace daga inda nake a zaune sai lokacin yai
ajiyan zuciya bai dai yi magana ba.
Maimakon mu tafi gida sai wani hanya ya dauka da mu can hanyan masarauta.
Gurin kaman company sayar da motoci ne yana tsayawa naga mutane suna nufomu suna
gaiyar dashi daya bayan daya.
Amirace kawar shawaran shi da hira dama yace Amirah tace na,am yayana yace kin
san gurin nan tace ,a,a yayana yace kallo signboard din can ki karan ta muna
alokaci daya duk muka daga kan mu an rubuta da mayan haruffa kamar haka.
MAJI ENTERPRISISE da sauri kowan mu ke kallon shi a cikin mamaki maji suna kuma
kaman na majin mu?
Natane yace cikin rashin ko in kula ya fadi hakan gurin muke zagawa muna duban
motocin dake gurin latest masu kyau da tsada yakai mu wani layi yace ga layin na
mata da ake yayi nan mukai ta kallon motocin cikin mamaki.
Wanan tace ai wancan yafi kyau haka sukai tayi a tsakanin su naga wani assh color
nace amma wanan sai naga duk tafisu kyau kai amma dai Bintu baki san mota ba
wallahi nace ina kuwa zan san su anty daga jaki sai rakumi na sani dandamama doki.
Wani irin dariya suka samin ganin yamma yayi daga inda yake tsaye yanufo yana
fadin mujen ku magariba ya kusa yanzun.
Muna hanya maryam tasakani gaba da,sheri wai nace jaki da rakumai na sani dan
dama dama doki.
Shima dariya yai min yace bana fada maku yar kauye bace kunki yarda dani, Amira
tace ,a,a gaskiya yaya yanzun Bintu ta wuce irin bakauyan da kake nufi fa.
Yau gasgi harda rawa tayi a gaban mutane ida dane waya usa yasa Bintu rawa a
bainan jama,a haka.
Yace ai bata da kunyane ki shiga rawa gaban mutane kamar wata chuss can dake, da
sauri na dago kai muka hada ido a gaban motan da yake Amirah tace ai duk mune don
mun fita rawa ita da take wani yauki kaman a gaban saurayin ta take.
Kila yana gurinne tunda kukaga tayi hakan kin san yar tara samari ne ita bata da
kunya ai.
Ai duk rawan karya mukeyi da mukaga uwayen mu sun iso aikowa ya jaye gurin
gabadaya aka basu fili.
Ni dai har muka iso gida ban yi magana ba shiru nayi kada ya disgani yadda ya
saba yi.
Sallah muka fara gabatarwa tukun muka dawo falo muka zauna sai ga mama sun dawo
daga gidan bukin.
Sai faman yi mata sannu da zuwa mukeyi maryam tace maji yau munga abin mamaki
gidan saida mota da sunan ki wallahi.
Sunana kuma ?
Maryam tace wallahi maji har gurin yaya yakaimu mu gani muna ta mamaki.
Wayan Baba ne ke kiran mama a lokacin bayan ya tambaya dasun dawo tabashi amsa da
eh sun dawo tana gida yanzun haka.
Nanmuka ga ta mike ta fita daga dakin zuwa can mukaji hayaniya a tsakar gida
maryam tace kuyi shiru mu ji don Allah,
Kaman fada ake a tsakan gida muna ji muka kwasa zuwa waje da saurin mu Baba ne da
Umma yake ta ja mata Allah ya isa akan Nafisa tana mayar mashi da amsa.
Sabon tashin hankali sai ga Amirah tashigo gidan abuge ta ita tayi tatil kawayen
ta sun kawo ta kofan gida sun zube ta haka.
Ranan muga tashin hankali don Baba zubewa yayi kofan shi da sauri su mama suka
tare shi suna mashi fitara.
Yaya Sagir yana gida shi ya fara jibgan Nafisa baji bagani cikin bacin rai gida
sai koke koke sukeyi .
Itako sai tabara takeyi tana fadin magana irin nasu na yan maye bata fasa magana
ba shi kuma bai fasa dukan ta ba.
Abinka da yan uwan taka sai ganin su Amirah nayi suna rike shi suna bashi hakuri
yayi hakkuri kada ya halakata.
Yana barin dukanta utakuma Umma ta shiga jibbagan ta kamar an aiko ta tana kuka
gwanin ban tausayi da ita.
Maryam.takira yaya sadauki ina jin yana kusa shi yazo ya dakatar da Umma yana
bata hakkuri ya dauki Baba suka nufi asibiti dashi.
Haka muka zauna jigun jigun damu agidan babu dadi don harka ya lalace ranan baki
gaba daya ya mutu wa Umma.
Can mukaji tana kuka tana fadin wallahi bata yarda yiwa Nafisa akayi talalace
kaman yadda dan maishi ya lalace ita wallahi bata barwa Allah sai ta dauki fan sa.
Anyi daidai sun dawo da Baba lokacin hajiya kubura tace ji mahaukaciya kawai sai
ki matsa ai kaikayi koma kan mashekiya ce akan ku zai kare yan banza.
Nan kuma suka shiga sabon cacan baki a tsakanin su da mummy sai zage zage da tonon
asiri sukeyi.
Kai haba mummy ku tausayawa bawan Allah nan mana ku dubi halin da yake ciki da
wani zaiji da fitanan ku ko da abinda ke damun shi.
Sadaukine yake wa mummy magana tace ai na bari sadauki amma in Alhaji ya mutu
gidan nan da hjy Atika da diyan ta zamuyi kuka wallahi.
Yaran kawai gasu nan ba,a gama wani ba su jefa mutumi a wani yaya za aiyi mutum
yai lafiya haka ?
Muna shiga daki bamu jima ba mama ta shigo dakin ita ma ta zauna jiki ba karfi
tare da ajiyan zuciya.
Tace ni fitinan gidan nan wallahi ya fara isata abu tun ana da jajjayen sawu har
girma yazi baza,a daina ba.
Tun farko shiyasa ban so zama ba wallahi babane ta tauyeni wai na zauna na saman
ma sadauki abokan shawara a gida shine kukaga har nakai war haka a gidan nan.
Mani mukan ai gara da kika zauna da bamusan inda za,a haife mu ba kuma inji
maryam cikin dariya.
Mama ta harare tace wawiya kawai don baki san irin wahalan dana fito cikin shi ba
ko ?
Mama al,amarinki kaman na mamana,wallahi haka sukai ta,kwasa da mama ta bawa har
mamana tagaji tabar mata gidan gashi ko yanzun dai sai hakali.
Maji tace haka abin yake yanzun ai a hanaka zaman lafiya gidan mijin ka in
bakakai zuciya nesa ba sai ka bar gurin gaban kuma da kake hange sai dace.
Tambayam bazata mama ta jefo min daidai lokacin da na daga kaina sama ina tunanen
halinda mahaifiyana take ciki a can kauye.
Wanan tunanen bayau na farashi ba walau in naji dadi ko naga wani abinda ya
danganta da rayuwan ta.
Muryan mama tana ce min Fatima yayan ku ya shigo yaci abincin shi kuwa yau ?
Da sauri na dago kai ina kallon ta don tambayan ani ya bani mamaki nace ina ganin
baici ba don tunda muka dawo banga ya shigo ba.
Tace dubo min shi a,waje ko yanan nai magana dashi naji may zai ba su baban ku
gudun mawan buki?
Namike tare da zura takalmina ganin a cikin gida zan tsaya sai ban saka hijjab
dina na ba nafita haka nan.
Na duba waje baya nan kaman nakoma na fada mata sai nace bari na leka dakin shi
tunda naga wuta a bude.
Na leka sai naga kamar bai ciki hakan yasa na dan kara takawa ciki zaune yake
yana shakan wani abu a wabi farin takarda haka.
Jin motsina yasa shi saurin dago kan shi da sauri mukai ido biyi da sauri na juya
zanbar dakin.
Abinka ga dan kwallo tako data ya cafko ni sai jikin shi ta baya zan saka ihu ya
danne